Gwamnatin tarayya ta ce, da yiwuwar Najeriya ta ci gaba da ciyo bashi, domin ci gaba da biyan tallafin man fetur.
Mai magana da yawun shugaban kasa, Femi Adesina, ne ya bayyana hakan yayin da ya ke magana ta cikin shirin Sunrise Daily na gidan talabijin na Channels TV da safiyar Laraba.
A cewrsa: “Ko ma dai yaya ne dole ne Najeriya ta ji a jikinta. Ko dai mu É—anÉ—ana kuÉ—armu a matsayinmu na ‘yan Æ™asa…ko kuma gwamnati ta ci gaba da ciyo bashi, wanda ba zai yi wa gwamnatin tarayya da jihohi kyau ba a tattalin arziki.
“Kun san irin yawan kuÉ—in da za a adana idan aka soke tallafin sannan kuma a saka su cikin wani fannin na Æ™asa. Idan ba a yi hakan ba a yanzu – na yarda ba abu ne mai sauÆ™i ba a yanzu – to fa dole ne mu É—anÉ—ana kuÉ—armu.”
A shekarar da ta gabata Majalisar Dattawa ta amince wa gwamnatin Buhari ta ciyo bashi iri-iri, ciki har da na dala biliyan 6.1, sai kuma na dala biliyan 16 da wani na yuro biliyan É—aya a watannin Yuli da Nuwamba kowannensu.
Akwai yiwuwar gwamnati ta kashe naira tiriliyan biyu da rabi cikin shekara É—aya da rabi da gwamnatin ta ce za ta ci gaba da biyan tallafin. A cewar BBC.