fidelitybank

KDC ta fara wayar da kan malaman Tsangayu a Kano

Date:

Wata Kungiya mai zaman kanta da ke fafutukar kawo sauyi ga tsarin Ilimi na Almajiri, KDC Foundation, ta dauki nauyin malaman Makarantun Tsangaya, domin tattaunawa da wayar da kan su kan sabon manhajar da ta tsara na tafiyar da makarantun Tsangaya.

Tattaunawar wadda ta gudana a ranar Litinin a Kano, tare da masu ruwa da tsaki daga gwamnatin tarayya da na jiha da malaman makarantu da kafafen yada labarai wanda ya ta ta’allaka ne kan hanyoyin zaburar da malaman Islamiyya, domin su amince da sauye-sauye masu kyau daga manhajar karatu.

Solacebase ta rawaito cewa, shugaban gidauniyar, Khalifa Muhammad Dankadai, ya ce, makasudin taron shi ne domin jin ta bakin malaman Islamiyya kan yadda suke kallon manhajar da kuma samun abubuwan da suka dace, domin tsara yadda ya dace da ra’ayinsu.

Ya ce “Ta hanyar nazarin abubuwan da malaman Islamiyya suka bayar, an tabbatar da cewa sun amince da tsarin kuma a shirye suke su yi aiki da shi a duk lokacin da aka samu wanda shi ne babban damuwarmu. Domin dole ne su yarda kuma su yi aiki tare da tsarin karatun sannan za mu cimma burinmu na gyara tsarin.

“Don haka za mu yi la’akari da ra’ayoyinsu tare da ba su hannu ‘yanci, domin gudanar da tsarin da kansu. Daga cikin abin da za mu yi shi ne koyar da Turanci da Lissafi, da kuma koyar da yara kanana sana’o’in kasuwanci ta yadda za su daina barace-barace a kan tituna da kuma yin ado da kyau kamar sauran daliban,” inji shi.

nigerian news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farashin Shinkafa zai cigaba da sauka – BUA

Shugaban rukunin kamfanonin BUA, Abdul Samad Rabiu, ya alƙawarta...

An kashe mutane 10 a wani sabon rikici da ya ɓarke a Filato

Aƙalla mutabe 10 ne aka kashe tare da sace...

Duk da sauƙin da aka samu har yanzu Abuja na fuskantar hauhawar farashi

Duk da cewa hukumar ƙididdiga ta ƙasa NBS, ta...

Hauhawar farashi ya ragu da kaso 23.71 a Najeriya – NBS

An samu raguwar hauhawar farashin kayayyaki a Najeriya daga...

Fiye da mutane 100 Makiyaya aka kashe a Jos

An ruwaito cewa an kashe wani makiyayi guda da...

Tinubu ka kori shugaban JAMB – Sowore

Dan siyasa mai fafutuka, Omoyele Sowore, ya yi kira...

Majalisa ta yi watsi da ƙudirin karɓa-karɓa

Majalisar wakilai ta yi watsi da wani ƙudirin doka...

Labarin mu na kaiwa Ƴan Bindiga abinci ƙarya ne – Ƴansanda

Rundunar ƴansandan Najeriya ta musanta rahotannin da ake yaɗawa...

Ba za mu yarda mu mutu a cikin PDP ba shi yasa muka koma APC – Sanatoci

Sanatocin Najeriya uku da suka fito daga jihar Kebbi,...

Sojoji sun tarwatsa wajen da ake hakar man fetur ba bisa ka’ida ba a Rivers

Rundunar Sojin Ruwa ta Najeriya, NNS, Pathfinder, ta tarwatsa...

Dan Tinubu Seyi da sauran ‘yan Siyasa sun fara neman kujerar gwamnan Legas

Siyasar Legas na kara ruruwa na neman maye gurbin...

Mayakan IS sun yi wa Sojojin Najeriya barna a kwana biyu

Mayaƙan IS sun ƙara kai wa sojojin Najeriya hari,...
X whatsapp