fidelitybank

Ranar 17 ga watan Maris za a fara sauraron daukaka karar Inusa Yellow

Date:

Kotun daukaka kara da ke garin Fatakwal ta sanya ranar 17 ga watan Maris, domin fara sauraron karar da Yunusa Yellow ya daukaka a gabanta na kalubalantar hukuncin babbar kotun jihar Bayelsa.

Lauyoyin Yunusa Yellow, Sunusi Musa ne ya sanar da hakan a shafinsa na Facebook ranar Talata.

Sauran lauyiyon da za su tsayawa Yunusa Yellow sun hadar da Huwaila Muhammad da Abdul Muhammad Rafindadi, da kuma Kayode Olasebikan.

Idan za a iya tunawa tun a shekarar 2015 ne aka kama Yunusa Yellow bisa zargin sato wata yarinya Ese Oruru da ga jihar Bayelsa zuwa Kano.

Yunusa Yellow dai ya taho da yarinyar Ese ne zuwa Kano suka kuma yi aure, sai dai an kama shi da laifin satar mutane da kuma safarar kananan yara.

Bayan kama shi ne a nan Kano aka kuma aike da shi can jihar Bayelsa garin da yarinyar ta ke domin a yanke masa hukunci.

Babbar kotun jihar dai ta zargeshi da laifuka har guda biyar da suka hadar da garkuwa da mutane da hakkewa karamar yarinya, da kuma yin amfani da dama kan karamar yariwa, sai kuma laifin yin amafani da karancin shekarunta wajen yi mata wayo. Saboda hakan ne kotun ta yanke masa hukuncin daurin shekaru 26 a gidan yari a can Bayelsa.

Sai dai da yake yanke hukunci alkalin kotun, Jane Inyanga, ta ce, Yunusa bai aikata laifi na farko ba wato garkuwa da mutane.

nasarawa news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Shettima ya yi wa iyalan marigayi Muhammadu Buhari ta’aziyya a Landan

Mataimakin shugaban Najeriya Kashim Shettima ya yi wa wasu...

Indiya na jimamin mutuwar Buhari – Modi

Firaministan India Narendra Modi, ya shiga jerin shugabanni da...

Kungiyar Gwamnoni sun bayar da hutu kan mutuwar Buhari

Ƙungiyar gwamnonin arewa maso yammacin Najeriya sun bayyana kaɗuwarsu...

Tinubu ya bayar da hutu don yin ta’azziyar Buhari

Gwamnatin tarayya ta ayyana gobe Talata, 15 ga watan...

Shettima ya isa Landan domin dawo da gawar marigayi Muhammadu Buhari

A safiyar yau Litinin ne mataimakin shugaban Najeriya Kashim...

Najeriya ta yi rashin Buhari – Obasanjo

Tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo, ya bayyana rasuwar tsohon...

Tabbas Buhari mutum ne mai kyakyawan halaye mai kishin kasa – IBB

Tsohon shugaban mulkin soji a Najeriya, Janar Ibrahim Babangida,...

Tabbas Buhari dan kishin kasa ne – Tinubu

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya bayyana tsohon Shugaban Ƙasa,...

Najeriya ta yi rashin Dattijo – Atiku Abubakar

Tsohon Mataimakin Shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya bayyana Muhammadu...

Buhari ya yi rayuwa mai sauki – Tajudeen

Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya Tajudeen Abba ya miƙa ta'aziyyar...

A Daura za a yi jana’izar Buhari – Radda

Gwamnan Katsina Dikko Umaru Radda ya ce iyalan Muhammadu...

Ƴan Najeriya na cece-kuce dangane da rasuwar Muhammadu Buhari

Mutuwar shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ta bar cece-kuce ga...
X whatsapp