fidelitybank

Jami’an tsaro sun kama masu laifi da muggan makamai

Date:

Rundunar sashen ‘yan sanda na musamman ta kasa, ta ce sun kama wasu da ke zargin masu satar mutane domin karbar kudin fansa da kuma ‘yan fashi, tare da masu safarar muggan makamai da muggan ƙwayoyi, da satar motoci a iyakokin kasar da kuma fyaɗe da suransu.

Rundunar ta tabbatar da hakan ne a acikin wata sanarwa da ta fitar mai kunshe da hannun ta aka kuma rabawa manema labarai.

Rundunar ‘yan sandan ta ce sun sami nasarar ƙwace bindiga samfurin AK47 guda 18 samfurin GPMG uku, da Ribalba biyu, da karamar bindiga guda, da alburusai 453 da kuma motoci 17 da suka yi fashinsu.

Cikin wadanda aka kama akwai shahararrun ‘yan fashin da ke satar motoci a jihohin Nasarawa da Abuja da Kebbi da Zamfara da Fatakwal.

Motocin da suka sata suna tsallakawa da su iyakar Najeriya da Jamhuriyar Nijar domin sayar da su ga wani mutum Alhaji Garba da har yanzu ake nema.

‘Yan sandan kasa da kasa ke aiki da takwarorinsu na Jamhuriyar Nijar, domin gano mutumin da masu taimaka masa, tuni suka gurfanar da su gaban shari’a.

Rundunar ta ce akwai wani matashi mai suna, Dayyabu Muhammad mai shekara 27 dan karamar hukumar Soba da ke jihar Kaduna, da aka samu da bindiga AK47 biyar da alburusai 250 a hannunsa.

BBC ta rawaito cewa, an kama shi ne a samamen da suka kai wa ɓarayin daji a Saminaka da ke jihar Kaduna, kuma bincike ya nuna Dayyabu ne yake kai wa ɓarayin muggan makamai.

today nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...

A sake sabon tsarin shugabancin INEC a Najeriya – Goodluck

Tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan, ya yi kira da...

Magoya bayan West Ham ku hada kai da Bowen – Potter

Mai horas da West Ham, Graham Potter ya bukaci...

Alhaki na ne kifewar jirgin kasa – Shugaban Hukumar

Shugaban hukumar jiragen ƙasa ta Najeriya (NRC), Kayode Opeifa,...

Tinubu ya haramta fitar da ɗanyen man kaɗanya

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya bayar da umarnin dakatar...

Hisba ta karɓi ƙorafe-ƙorafe 83,776 a Kano

Rundunar Hisbah ta jihar Kano ta bayyana cewa, a...

Ganduje ba dan cin hanci ba ne – Martanin Garba Ga Gwamnatin Kano

Tsohon kwamishinan yaɗa labarai na Jihar Kano, Muhammad Garba,...

Kungiyar Malaman Jami’o’i bangaren BUK sun yi zanga-zangar Lumana

Kungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU), reshen Jami’ar Bayero Kano (BUK),...
X whatsapp