fidelitybank

Jami’an tsaro sun kama masu laifi da muggan makamai

Date:

Rundunar sashen ‘yan sanda na musamman ta kasa, ta ce sun kama wasu da ke zargin masu satar mutane domin karbar kudin fansa da kuma ‘yan fashi, tare da masu safarar muggan makamai da muggan ƙwayoyi, da satar motoci a iyakokin kasar da kuma fyaɗe da suransu.

Rundunar ta tabbatar da hakan ne a acikin wata sanarwa da ta fitar mai kunshe da hannun ta aka kuma rabawa manema labarai.

Rundunar ‘yan sandan ta ce sun sami nasarar ƙwace bindiga samfurin AK47 guda 18 samfurin GPMG uku, da Ribalba biyu, da karamar bindiga guda, da alburusai 453 da kuma motoci 17 da suka yi fashinsu.

Cikin wadanda aka kama akwai shahararrun ‘yan fashin da ke satar motoci a jihohin Nasarawa da Abuja da Kebbi da Zamfara da Fatakwal.

Motocin da suka sata suna tsallakawa da su iyakar Najeriya da Jamhuriyar Nijar domin sayar da su ga wani mutum Alhaji Garba da har yanzu ake nema.

‘Yan sandan kasa da kasa ke aiki da takwarorinsu na Jamhuriyar Nijar, domin gano mutumin da masu taimaka masa, tuni suka gurfanar da su gaban shari’a.

Rundunar ta ce akwai wani matashi mai suna, Dayyabu Muhammad mai shekara 27 dan karamar hukumar Soba da ke jihar Kaduna, da aka samu da bindiga AK47 biyar da alburusai 250 a hannunsa.

BBC ta rawaito cewa, an kama shi ne a samamen da suka kai wa ɓarayin daji a Saminaka da ke jihar Kaduna, kuma bincike ya nuna Dayyabu ne yake kai wa ɓarayin muggan makamai.

legitnewsnigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...
X whatsapp