fidelitybank

EXPO 2020: Buhari ya tafi kasar hadadiyar Daular Larabawa

Date:

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bar Abuja domin halartar bikin EXPO 2020 Dubai da ke Hadaddiyar Daular Larabawa a ranar Laraba.

Wata sanarwa dauke da sa hannun mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin yada labarai, Femi Adesina, wanda PlatinumPost ta samu, ta bayyana cewa, Buhari zai halarci taron bikin EXPO 2020 a Dubia.

Mista Adesina ya bayyana cewa, “EXPO 2020 Dubai, taren mai taken, “Wayar da kan al’umma, domin samun kyakyawar gobe”, ya samar da yanayin da Najeriya za ta shiga cikin ƙasashe sama da 190 domin kulla haɗin gwiwa na gaskiya da ma’ana “domin gina kyakkyawar makoma ga kowa da kowa. Bikin baje kolin zai sake baiwa tawagar Najeriya wata dama ta nuna gagarumin ci gaban da aka samu a fannin tattalin arziki a cikin shekaru shidan da suka gabata a matsayin ginshikin mayar da kasar nan muhimmiyar makoma ta zuba jari kai tsaye daga ketare”.

Shugaban kasar zai samu rakiyar ministocin harkokin waje, Geoffrey Onyeama, masana’antu, Ciniki da Zuba Jari, Otunba Adeniyi Adebayo, Kudi, kasafin kudi da tsare-tsare na kasa, Hajia Zainab Shamsuna Ahmed,  Tsaro, Manjo. Janar, Bashir Magashi (mai ritaya), Jirgin sama, Sanata Hadi Sirika, Noma da Raya Karkara, Dr. Mohammad Abubakar da dai sauran tawagar jami’an gwamnati.

guardian newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mu na aiki tuƙuru wajen daƙile ayyukan ta’adda a Najeriya – Christopher Musa

Babban hafsan tsaron Najeriya, Janar Christopher Musa, ya tabbatarwa...

Mayaƙan ISWAP sun harbe Manoma 23 a Borno

Rahotanni sun bayyana cewa ƙungiyar mayaƙan ISWAP ta kashe...

Real Madrid ta ɗauki ɗan wasan baya daga Bournemouth

Real Madrid ta sanar da sayen ɗan wasan baya...

Gwamnatin Kano ta haramta yin bikin Ƙauyawa da gidajen biki

Hukumar tace fina-finai a jihar Kano ta sanar da...

An kashe ƴan Boko Haram biyar a Borno

Dakarun sojin Najeriya haɗe da wasu maharba sun daƙile...

Farashin Shinkafa zai cigaba da sauka – BUA

Shugaban rukunin kamfanonin BUA, Abdul Samad Rabiu, ya alƙawarta...

An kashe mutane 10 a wani sabon rikici da ya ɓarke a Filato

Aƙalla mutabe 10 ne aka kashe tare da sace...

Duk da sauƙin da aka samu har yanzu Abuja na fuskantar hauhawar farashi

Duk da cewa hukumar ƙididdiga ta ƙasa NBS, ta...

Hauhawar farashi ya ragu da kaso 23.71 a Najeriya – NBS

An samu raguwar hauhawar farashin kayayyaki a Najeriya daga...

Fiye da mutane 100 Makiyaya aka kashe a Jos

An ruwaito cewa an kashe wani makiyayi guda da...

Tinubu ka kori shugaban JAMB – Sowore

Dan siyasa mai fafutuka, Omoyele Sowore, ya yi kira...

Majalisa ta yi watsi da ƙudirin karɓa-karɓa

Majalisar wakilai ta yi watsi da wani ƙudirin doka...
X whatsapp