fidelitybank

Jami’an tsaro sun kama masu laifi da muggan makamai

Date:

Rundunar sashen ‘yan sanda na musamman ta kasa, ta ce sun kama wasu da ke zargin masu satar mutane domin karbar kudin fansa da kuma ‘yan fashi, tare da masu safarar muggan makamai da muggan ƙwayoyi, da satar motoci a iyakokin kasar da kuma fyaɗe da suransu.

Rundunar ta tabbatar da hakan ne a acikin wata sanarwa da ta fitar mai kunshe da hannun ta aka kuma rabawa manema labarai.

Rundunar ‘yan sandan ta ce sun sami nasarar ƙwace bindiga samfurin AK47 guda 18 samfurin GPMG uku, da Ribalba biyu, da karamar bindiga guda, da alburusai 453 da kuma motoci 17 da suka yi fashinsu.

Cikin wadanda aka kama akwai shahararrun ‘yan fashin da ke satar motoci a jihohin Nasarawa da Abuja da Kebbi da Zamfara da Fatakwal.

Motocin da suka sata suna tsallakawa da su iyakar Najeriya da Jamhuriyar Nijar domin sayar da su ga wani mutum Alhaji Garba da har yanzu ake nema.

‘Yan sandan kasa da kasa ke aiki da takwarorinsu na Jamhuriyar Nijar, domin gano mutumin da masu taimaka masa, tuni suka gurfanar da su gaban shari’a.

Rundunar ta ce akwai wani matashi mai suna, Dayyabu Muhammad mai shekara 27 dan karamar hukumar Soba da ke jihar Kaduna, da aka samu da bindiga AK47 biyar da alburusai 250 a hannunsa.

BBC ta rawaito cewa, an kama shi ne a samamen da suka kai wa ɓarayin daji a Saminaka da ke jihar Kaduna, kuma bincike ya nuna Dayyabu ne yake kai wa ɓarayin muggan makamai.

daily post nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za mu ɗauki matakin hana sake faruwar kisan mutane – Gwamnatin Filato

Gwamnatin jihar Filato ta jaddada aniyarta ta ɗaukar mataki...

Babu barazanar tsaro a Abuja – Najeriya

Gwamnatin Tarayya ta ce, babu wata barazanar a babban...

Isra’ila za ta mayarwa da Iran martani duk da tsagaita wuta

Ministan tsaron Isra'ila, Katz ya bayyana cewa, ya ba...

Ba mu kai wa Isra’ila hari ba – Iran

Kafar watsa labarai ta Iran ta ruwaito gwamnatin ƙasar...

Duk da faduwar farashin mai NNPCL ya kara farashi

Kamfanin man fetur na Najeriya, NNPCL ya ƙara farashin...

Duk wasu ƙawayen Amurka za su ɗanɗanar kuɗarsu – Iran

Rundunar dakarun juyin juya halin Iran ta fitar da...

Iran ta mayar da martani kan sojojin Amurka dake Qatar

Kafofin yaɗa labaran Iran sun bayyana cewa ƙasar ta...

Faransa ba ta goyon bayan Amurka na kifer da gwamnatin Iran – Barrot

Ministan harkokin wajen Faransa ya ce, ƙasarsu ba ta...

Kotu a Kano ta ɗaure masu satar Yara

Babbar kotun jihar Kano da ke zamanta a Miller...

Ba wata hujja da Amurka za ta kai wa Iran hari – Rasha

An gudanar da tattaunawa tsakanin shugaban Rasha Vladimir Putin...

Tinubu ya miƙa saƙon ta’aziyya ga mutanen Kano da Kaduna da Borno

Shugaba Bola Tinubu ya yi Alla-wadai da kisan wasu...

Amurka ta tafka babban kuskure – Iran

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya yi Alla-wadai...
X whatsapp