Gwamnan jihar Borono, Babagana Umara Zulum, ya baiwa sojojin Najeriya da mayakan ISWAP, su ka jikkata Naira miliyan Biyar.
‘Yan ta’addan sun kai wani hari ne a Rann da ke iyaka da Najeriya da kuma kasar Kamaru a Kala Balge da ke karamar hukumar jihar Borno.
Jaridar Dailytrust ta rawaito cewa, Zulum ya mika kudin ne domin su raba a lokacin da ya ziyarce su a asibitin Sojoji a Maimalari da ke jihar.
Zulum ya samu tarba daga babban jami’I mai kula da runduna ta Bakwai, Birgediya Janar Abdulwaha Eyitayo.