fidelitybank

Gwamnatin Kebbi ta yi hadin gwiwa da Likitocin kasa da kasa

Date:

Kungiyar likitoci mai zaman kanta ba tare da iyaka ba ta kasa da kasa ta kasar Faransa, (Doctors without Borders) ta ce a shirye ta ke ta hada gwiwa da gwamnatin jihar Kebbi, domin isar da ayyukan kiwon lafiya ga al’ummar jihar.

Gwamnan jihar Kebbi, Abubakar Atiku Bagudu ne ya karbi bakwancin tawagar karkashin jagorancin shugaban tawagar, Dr Shaukat Muttaqi a gidan gwamnati dake Birnin Kebbi.

A lokacin da ya ke karbar tawagar,  a madadin gwamnan, shugaban ma’aikatan jihar, Alhaji Sulaiman Muhammad Argungu, ya yi maraba da likitocin tare da bayyana farin cikinsa dangane da shirye-shiryen sanya hannu kan yarjejeniyar (MOU) da hadin gwiwa da gwamnati.

Ya kuma tabbatar wa da tawagar cewa, gwamnatin jihar Kebbi za ta samar da yanayi mai kyau, domin gudanar da aikin yadda ya kamata wajen samun kyakkyawan aiki.

Shugaban tawagar, Dr. Shaukat Muttaqi ya bayyana cewa, makasudun ziyarar ta su ita ce, tattauna muhimman ayyukan da suka kiwon lafiya da shirin samar da abinci mai gina jiki da kuma kula da matsalolin al’umm a jihar Kebbi.

A cewarsa, kungiyar Doctors without Borders ta dukufa wajen samar da ayyukan jinya kyauta ga al’ummar jihar Kebbi a shirinta na watanni shida na farko tare da fatan cimma yarjejeniya da ma’aikatar lafiya da jihar Kebbi, domin fara ayyuka cikin gaggawa.

punch news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp