fidelitybank

Gwamnati ta kawo karshen kisan gillar da a ke yi wa ‘yan Najeriya – Sheikh Dahiru Bauchi

Date:

Fitaccen malamin addinin musulunci a Najeriya, Sheikh Dahiru Usman Bauchi, ya bukaci gwamnatin tarayya ta yi duk mai yiwuwa wajen kawo karshen ayyukan ’yan ta’addar da su ka addabi Najeriya.

Sheikh Dahiru Bauchi ya kuma bayyana wajibcin gwamnati ta fitar da ’yan Najeriya daga halin tsoron da suke ciki, a lokacin da ya ke jawabi a majalisinsa, inda ya bayyana takaicinsa kan halin rashin tsaron da Najeriya ke ciki.

Ya bayyana cewa, “Ba mu zabe su don mu zama haka ba, ba mu zabe su don mu zama abin tausayi irin wannan ba, ya zama ana kashe mu ba mai kariya ana sayar da mu kamar dabbobi — ana yin abin da aka ga dama da mu — alhali muna da gwamnatoci har guda uku a kanmu; Wannan abin kunya ne, abin dariya ne, abin kuka ne”.

Jawabin malamin na zuwa ne kwanaki kadan bayan kisan gillar da ’yan bindiga suka yi wa sama da mutun 30 a Sabon Birni a Jihar Sokoto, wanda ya haifar da zanga-zanga a Arewacin Najeriya.

’Yan bindiga sun dauki tsawon lokaci suna kashe-kashe da garkuwa da mutane domin karbar kudaden fansa, gami da yi wa mata fyade da kona garuruwa da dukiyoyi da sauran na’uikan ta’addanci, musamman a yankin Arewa maso Yammacin Najeriya.

Sheikh Dahiru Bauchi ya ce, “Abin da yake wajibi ga gwamnatoci [shi ne] su kula su fitar da mu daga abin da muke ciki na tsoro —kana gidanka kana jin tsoro, kana waje kana jin tsoro, kana tafiya kana jin tsoro, alhali akwai gwamnatoci har guda uku a kanka.”

“Duk muna daura muku nauyi na kuwala da rayukan jama’ar Najeriya da zaman lafiyar Najeriya da walwalar Najeriya; Ina aka ce kasa ko noma ba za a yi ba, to me za a ci?”

Ya yaddada kira ga gwamnatin tarayya da ta jihohi da kananan hukumomi su tashi tsaye, domin yin duk abin da ya dace wajen samar da tsaro da kuma sauke duk nauyin da kundin tsarin mulki ya rataya a wuyansu na kare rayuka da dukiyoyi da kuma jin dadin al’ummar kasa. A cewar Aminiya.

 

legit

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farashin Shinkafa zai cigaba da sauka – BUA

Shugaban rukunin kamfanonin BUA, Abdul Samad Rabiu, ya alƙawarta...

An kashe mutane 10 a wani sabon rikici da ya ɓarke a Filato

Aƙalla mutabe 10 ne aka kashe tare da sace...

Duk da sauƙin da aka samu har yanzu Abuja na fuskantar hauhawar farashi

Duk da cewa hukumar ƙididdiga ta ƙasa NBS, ta...

Hauhawar farashi ya ragu da kaso 23.71 a Najeriya – NBS

An samu raguwar hauhawar farashin kayayyaki a Najeriya daga...

Fiye da mutane 100 Makiyaya aka kashe a Jos

An ruwaito cewa an kashe wani makiyayi guda da...

Tinubu ka kori shugaban JAMB – Sowore

Dan siyasa mai fafutuka, Omoyele Sowore, ya yi kira...

Majalisa ta yi watsi da ƙudirin karɓa-karɓa

Majalisar wakilai ta yi watsi da wani ƙudirin doka...

Labarin mu na kaiwa Ƴan Bindiga abinci ƙarya ne – Ƴansanda

Rundunar ƴansandan Najeriya ta musanta rahotannin da ake yaɗawa...

Ba za mu yarda mu mutu a cikin PDP ba shi yasa muka koma APC – Sanatoci

Sanatocin Najeriya uku da suka fito daga jihar Kebbi,...

Sojoji sun tarwatsa wajen da ake hakar man fetur ba bisa ka’ida ba a Rivers

Rundunar Sojin Ruwa ta Najeriya, NNS, Pathfinder, ta tarwatsa...

Dan Tinubu Seyi da sauran ‘yan Siyasa sun fara neman kujerar gwamnan Legas

Siyasar Legas na kara ruruwa na neman maye gurbin...

Mayakan IS sun yi wa Sojojin Najeriya barna a kwana biyu

Mayaƙan IS sun ƙara kai wa sojojin Najeriya hari,...
X whatsapp