Wata gobara ta ƙone tarin kaya da abinci da kuɗin su ya haura Naira miliyan uku da rabi a unguwar Lokan Maƙera ƙaramar hukumar Gwale da ke birnin Kano.
Da ya ke jawabi ga manema labarai, mai gidan, Malam Sulaiman Abdullahi Lokon Makera, ya bayyana cewa, wutar ta tashi da misalin ƙarfe biyu na rana, sakamakon wutar lantarki mai ƙarfi.
Ya ce, “Wutar ta ƙone kayan sawa da kayan abinci da muhimman takardu da rufin ɗakuna guda huɗu, sai dai babu wanda ya jikkata a cikin mu”.
Tuni dai hukumar ba da agajin gaggawa ta jihar Kano ƙarƙashin shugaban hukumar Dr. Sale Aliyu Jilli, ta ziyarci gidan tare da kai gudunmawar kayan abinci da kayan rufin kwano da siminti da katifu domin rage masa raɗadi.
Hukumar bayar da agajin gaggawar, ta kuma yi kira ga sauran al’umma da su rinka kiyaye wa da kayayyakin wuta musamman a wannan lokaci na hunturu.