Wani ɗalin makaranta mai shekara 16 a kasar Afirka ta Kudu ya harbe ɗan ajinsu, biyo bayan wata rigima tsakaninsu, inda daga baya ya kashe kan sa shima.
Yaran suna mataki na 10 a Sakandaren Lesiba da ke Daveyton.
sai dai hukumomi sun ce an yi harbin ne ranar Laraba yayin da a ka koma sabon zangon karatu.
ya zuwa yanzu dai ‘yan sanda na gudanar da bincike kan lamarin, kuma an tura jami’an kula da lalurar ƙwaƙwalwa da zimmar duba lafiyar waɗanda abin ya ritsa da su.