fidelitybank

Garkuwa da Mutane: Jami’ar Abuja ta dauki ‘yan sintiri da ‘yan Banga da mafarauta

Date:

Jami’ar Abuja ta kaddamar da aikin sintiri na awa 24 a cikin harabarta da kewaya ta hanyar amfani da mafarauta da ’yan banga, domin dakile ayyukan ’yan bindiga.

Uban Jami’ar Abuja, Modibbo Mohammed, ya ce an dauki matakin ne bayan harin ’yan bindiga da suka yi garkuwa da wasu ma’aikata a rukunin gidajensu da ke cikin jami’ar.

Ya ce,“Mun dauki mafarauta da ’yan banga su rika gudanar da sintiri a yankin da babu Katanga, saboda filin jami’ar na da girma sosai,” inji shi.

Amiya ta rawaito cewa, Uban Jami’ar Abuja ya shaida wa taron manyan shugabanni da jami’an gudanarwa da na kungiyoyin jami’ar, cewa su na yin duk mai yiwuwa, domin ganin ba a sake kai hari ba a jami’ar.

Da ya ke magana game da halin da gidajen ma’aikatan jami’ar su ke ciki, ya ce, “Gidajen ma’aikatan mu ba su kai yadda ake bukata ba, har kunya na ke ji game da irin gidajen da ma’aikatanmu ke zaune a ciki. Kwamitin gudanarwar Jami’ar ya yi zama da Ministan Abuja a kan lamarin, kuma ministan ya yi alkawarin daukar mataki a kai, nan ba da jimawa ba. Nan gaba kadan kuma za mu tura wakilanmu zuwa hukumar FERMA, domin ta bayar da muhimmanci wajen gyara hanyoyin da ke cikin jami’ar,” inji Modibo.

vanguard newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Yadda aka gudanar da addu’o’in Buhari a Villa

A ranar Alhamis ne aka gudanar da addu'o'i ga...

Rasha tarnaki ce a wajen Tarayyar Turai – Jamus

Shugaban gwamnatin Jamus Friedrich Merz ya shaidawa BBC cewa...

Amurka ba ta goyon bayan Isra’ila a harin Syria – Trump

Amurka ta ce ba ta goyon bayan hare-haren da...

Tinubu zai zo Kano ta’aziyyar Dantata

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu zai kai ziyara Kano yau...

Tarayyar Turai tamince da ƙaƙaba wa Rasha sabbin takunkumai

Ƙungiyar Tarayyar Turai ta amince da ƙaƙaba wa Rasha...

Gwamnan Filato ya zargi Jami’ai da kin kama ‘yan bindiga

Gwamnatin jihar Filato ta zargi jami'an sojojin ƙasar da...

Za a yi wa Buhari addu’a a Abuja

Gwamnatin Tarayya za ta jagoranci gudanar da taron addu'o'i...

Buhari ya ban umarni na kula da Talakawan Najeriya – Peter Obi

Jagorar jam'iyyar LP a Najeriya, Peter Obi ya ce,...

Sojojin hadin gwiwa sun hallaka ‘yan Boko Haram a tafkin Chadi

Rundunar hadin gwiwa mai yaƙi da Boko Haram a...

Na yi rashin aboki na gari kuma Najeriya ta rasa mutumin kirki – Tinubu

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, na ci gaba da alhinin...

Shettima ya jagoranci yi wa Buhari addu’o’i na musamman a Daura

An gudanar da addu'o'i na musamman don neman gafara...

Isra’ila ta kashe mana fararen hula – Syria

Shugaban Syria, Ahmed al-Sharaa ya zargi Isra'ila da kai...
X whatsapp