fidelitybank

Garkuwa da Mutane: Jami’ar Abuja ta dauki ‘yan sintiri da ‘yan Banga da mafarauta

Date:

Jami’ar Abuja ta kaddamar da aikin sintiri na awa 24 a cikin harabarta da kewaya ta hanyar amfani da mafarauta da ’yan banga, domin dakile ayyukan ’yan bindiga.

Uban Jami’ar Abuja, Modibbo Mohammed, ya ce an dauki matakin ne bayan harin ’yan bindiga da suka yi garkuwa da wasu ma’aikata a rukunin gidajensu da ke cikin jami’ar.

Ya ce,“Mun dauki mafarauta da ’yan banga su rika gudanar da sintiri a yankin da babu Katanga, saboda filin jami’ar na da girma sosai,” inji shi.

Amiya ta rawaito cewa, Uban Jami’ar Abuja ya shaida wa taron manyan shugabanni da jami’an gudanarwa da na kungiyoyin jami’ar, cewa su na yin duk mai yiwuwa, domin ganin ba a sake kai hari ba a jami’ar.

Da ya ke magana game da halin da gidajen ma’aikatan jami’ar su ke ciki, ya ce, “Gidajen ma’aikatan mu ba su kai yadda ake bukata ba, har kunya na ke ji game da irin gidajen da ma’aikatanmu ke zaune a ciki. Kwamitin gudanarwar Jami’ar ya yi zama da Ministan Abuja a kan lamarin, kuma ministan ya yi alkawarin daukar mataki a kai, nan ba da jimawa ba. Nan gaba kadan kuma za mu tura wakilanmu zuwa hukumar FERMA, domin ta bayar da muhimmanci wajen gyara hanyoyin da ke cikin jami’ar,” inji Modibo.

daily post today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...
X whatsapp