Jami’ar Abuja ta kaddamar da aikin sintiri na awa 24 a cikin harabarta da kewaya ta hanyar amfani da mafarauta da ’yan banga, domin dakile ayyukan ’yan bindiga.
Uban Jami’ar Abuja, Modibbo Mohammed, ya ce an dauki matakin ne bayan harin ’yan bindiga da suka yi garkuwa da wasu ma’aikata a rukunin gidajensu da ke cikin jami’ar.
Ya ce,“Mun dauki mafarauta da ’yan banga su rika gudanar da sintiri a yankin da babu Katanga, saboda filin jami’ar na da girma sosai,” inji shi.
Amiya ta rawaito cewa, Uban Jami’ar Abuja ya shaida wa taron manyan shugabanni da jami’an gudanarwa da na kungiyoyin jami’ar, cewa su na yin duk mai yiwuwa, domin ganin ba a sake kai hari ba a jami’ar.
Da ya ke magana game da halin da gidajen ma’aikatan jami’ar su ke ciki, ya ce, “Gidajen ma’aikatan mu ba su kai yadda ake bukata ba, har kunya na ke ji game da irin gidajen da ma’aikatanmu ke zaune a ciki. Kwamitin gudanarwar Jami’ar ya yi zama da Ministan Abuja a kan lamarin, kuma ministan ya yi alkawarin daukar mataki a kai, nan ba da jimawa ba. Nan gaba kadan kuma za mu tura wakilanmu zuwa hukumar FERMA, domin ta bayar da muhimmanci wajen gyara hanyoyin da ke cikin jami’ar,” inji Modibo.