fidelitybank

Fim dina ba don mutanen Kano na yi ba – Daraktan fim din Makaranta

Date:

Daraktan fim din ‘Makaranta’ ya ce, bai damu da barazanar da hukumar tace fina-finan jihar Kano ba a kan kama shi da za ta yi.

Hukumar na neman, Aminu Umar Mukhtar ruwa a jallo, inda ta ke zargin sa da lalata tarbiyya da kuma rashin bin ka’ida yayin fitar da tallan fim din.

Fim din ‘Makaranta’ ya nuna abubuwa da dama da mutane da dama suke ganin ba su dace a yi a cikin fim din ba, wadanda su ka hada da madigo da batsa da makamatansu.

Hakan ne ya sa shugaban hukumar tace fina-finan ta Kano, Isma’ila Na’abba Afakallah, ya shaida wa BBC cewa, sun aika wa daraktan takardar gayyata a watan jiya, domin ya je gabansu ya yi musu bayani na dalilan da suka sa ya yi fim din ba tare da samun izininsu ba.

A cewarsa, Aminu Umar Mukhtar ya shaida musu cewa zai zo gabansu idan a ka shiga sabuwar shekara, amma bai je ba, lamarin da ya sa su ka fara nemansa ruwa a jallo.

Afakallah ya kara da cewa za su tuhumi daraktan fim din bisa laifukan da su ke ganin ya aikata.

Sai dai Aminu Umar Mukhtar ya ce”Ba Don mutanen Kano na yi fim din ba”.

Sai dai a tattaunawarsa da BBC, Aminu ya kare kansa bisa fitar da tallan fim din, ya na mai cewa,”Ban damu da neman da hukumar tace fina-finan Kano ke yin ba”.

“Na samu labarin cewa hukumar tace fina-finan Kano, ta na nema na. Ban yi ko gezau ba, domin kuwa ban aikata wani laifi ba,” in ji shi.

“Fim din da na yi ba a kan mutanen Kano ko Hausawa na yi ba, na yi amfani da harsuna 17 a cikinsa. Kuma ba a Kano a ka dauki fim din ba, domin haka ban san dalilin da ya sa ya zama abin ce-ce-ku-ce ba. Fim dina ba kawai ya na magana ba ne game da ilimin jima’i ba, ya na kuma nuna illolin kaciyar mata da wayar da kai kan abubuwan da ke faruwa a tsakanin Hausawa da ma wasu al’ummomi.” A cewar sa.

Daraktan fim din na ‘Makaranta’ ya musanta cewa wasu ne suke daukar nauyin sa, domin ya bata tarbiyyar mutane.

punch news paper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko ƴanƙwallon...

Sunderland ta ɗauko ƴanƙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ƙwallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...

Luiz Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool

Luis Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool...

NNPCL ya musanta sayar da matatar mai ta Fatakwal

Babban kamfanin man fetur na kasa, NNPCL ya musanta...

Mun samu kuɗin gina titin jirgi daga Maiduguri zuwa Abia – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ce, ta samu duka kuɗin gudanar...

Sanatocin Arewa sun yi tir da kisan Zamfara

Ƙungiyar sanatocin Arewa, ta yi Allah wadai da kisan...

Tattalin arzikin Najeriya zai kara bunkasa a shekarar nan – IMF

Asusun Bayar da Lamuni na Duniya, IMF ya sabunta...

Ma’aikatan jinya sun fara yajin aiki a Najeriya

Ƙungiyar ma'aikatan jinya da unguzomomi ta kasa, ta fara...

Birtaniya ta na tsantsanr goyon bayam Hamas ne kawai – Netanyahu

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, matakin da Birntaniy...

Birtaniya ta gindaya wa Isra’ila sharuɗa

Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya shimfiɗa wa Isra'ila wasu...
X whatsapp