fidelitybank

Fim dina ba don mutanen Kano na yi ba – Daraktan fim din Makaranta

Date:

Daraktan fim din ‘Makaranta’ ya ce, bai damu da barazanar da hukumar tace fina-finan jihar Kano ba a kan kama shi da za ta yi.

Hukumar na neman, Aminu Umar Mukhtar ruwa a jallo, inda ta ke zargin sa da lalata tarbiyya da kuma rashin bin ka’ida yayin fitar da tallan fim din.

Fim din ‘Makaranta’ ya nuna abubuwa da dama da mutane da dama suke ganin ba su dace a yi a cikin fim din ba, wadanda su ka hada da madigo da batsa da makamatansu.

Hakan ne ya sa shugaban hukumar tace fina-finan ta Kano, Isma’ila Na’abba Afakallah, ya shaida wa BBC cewa, sun aika wa daraktan takardar gayyata a watan jiya, domin ya je gabansu ya yi musu bayani na dalilan da suka sa ya yi fim din ba tare da samun izininsu ba.

A cewarsa, Aminu Umar Mukhtar ya shaida musu cewa zai zo gabansu idan a ka shiga sabuwar shekara, amma bai je ba, lamarin da ya sa su ka fara nemansa ruwa a jallo.

Afakallah ya kara da cewa za su tuhumi daraktan fim din bisa laifukan da su ke ganin ya aikata.

Sai dai Aminu Umar Mukhtar ya ce”Ba Don mutanen Kano na yi fim din ba”.

Sai dai a tattaunawarsa da BBC, Aminu ya kare kansa bisa fitar da tallan fim din, ya na mai cewa,”Ban damu da neman da hukumar tace fina-finan Kano ke yin ba”.

“Na samu labarin cewa hukumar tace fina-finan Kano, ta na nema na. Ban yi ko gezau ba, domin kuwa ban aikata wani laifi ba,” in ji shi.

“Fim din da na yi ba a kan mutanen Kano ko Hausawa na yi ba, na yi amfani da harsuna 17 a cikinsa. Kuma ba a Kano a ka dauki fim din ba, domin haka ban san dalilin da ya sa ya zama abin ce-ce-ku-ce ba. Fim dina ba kawai ya na magana ba ne game da ilimin jima’i ba, ya na kuma nuna illolin kaciyar mata da wayar da kai kan abubuwan da ke faruwa a tsakanin Hausawa da ma wasu al’ummomi.” A cewar sa.

Daraktan fim din na ‘Makaranta’ ya musanta cewa wasu ne suke daukar nauyin sa, domin ya bata tarbiyyar mutane.

punch newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...
X whatsapp