Tsohon shugaban kasa, Goodluck Ebele Jonathan, ya ziyarci shugaba Muhammadu Buhari a fadarsa a yau Alhamis.
A cewar mai magana da yawun fadar shugaban ƙasa, Femi Adesina, Jonathan ya yi wa Buhari jawabi game da halin da a ke ciki a siyasar ƙasar Mali.
Adesina ya ce,”Za a gudanar da taron ƙungiyar Ecowas na musamman a Ghana ranar Lahadi, domin tattauna matsalolin Mali, dalilin da ya sa Jonathan, a matsayinsa na manzo na musamman daga ƙungiyar Ecowas, ya ziyarci Buhari kenan”.
Ya ƙara da cewa, “Buhari ya jaddada matsayarsa cewa, duk wani mataki da Najeriya za ta ɗauka kan rikicin siyasar Mali za ta yi shi ne a madadin ECOWAS”.A cewar Adesina.
Tun farko Buhari ya karɓi baƙwancin wakili na musamman daga shugaban riƙon ƙwarya na Mali, Kanal Asimi Goita. Buhari ya yi alƙawarin cewa Najeriya za ta yi “bakin ƙoƙarinta” wajen taimaka wa Mali.