fidelitybank

Fim dina ba don mutanen Kano na yi ba – Daraktan fim din Makaranta

Date:

Daraktan fim din ‘Makaranta’ ya ce, bai damu da barazanar da hukumar tace fina-finan jihar Kano ba a kan kama shi da za ta yi.

Hukumar na neman, Aminu Umar Mukhtar ruwa a jallo, inda ta ke zargin sa da lalata tarbiyya da kuma rashin bin ka’ida yayin fitar da tallan fim din.

Fim din ‘Makaranta’ ya nuna abubuwa da dama da mutane da dama suke ganin ba su dace a yi a cikin fim din ba, wadanda su ka hada da madigo da batsa da makamatansu.

Hakan ne ya sa shugaban hukumar tace fina-finan ta Kano, Isma’ila Na’abba Afakallah, ya shaida wa BBC cewa, sun aika wa daraktan takardar gayyata a watan jiya, domin ya je gabansu ya yi musu bayani na dalilan da suka sa ya yi fim din ba tare da samun izininsu ba.

A cewarsa, Aminu Umar Mukhtar ya shaida musu cewa zai zo gabansu idan a ka shiga sabuwar shekara, amma bai je ba, lamarin da ya sa su ka fara nemansa ruwa a jallo.

Afakallah ya kara da cewa za su tuhumi daraktan fim din bisa laifukan da su ke ganin ya aikata.

Sai dai Aminu Umar Mukhtar ya ce”Ba Don mutanen Kano na yi fim din ba”.

Sai dai a tattaunawarsa da BBC, Aminu ya kare kansa bisa fitar da tallan fim din, ya na mai cewa,”Ban damu da neman da hukumar tace fina-finan Kano ke yin ba”.

“Na samu labarin cewa hukumar tace fina-finan Kano, ta na nema na. Ban yi ko gezau ba, domin kuwa ban aikata wani laifi ba,” in ji shi.

“Fim din da na yi ba a kan mutanen Kano ko Hausawa na yi ba, na yi amfani da harsuna 17 a cikinsa. Kuma ba a Kano a ka dauki fim din ba, domin haka ban san dalilin da ya sa ya zama abin ce-ce-ku-ce ba. Fim dina ba kawai ya na magana ba ne game da ilimin jima’i ba, ya na kuma nuna illolin kaciyar mata da wayar da kai kan abubuwan da ke faruwa a tsakanin Hausawa da ma wasu al’ummomi.” A cewar sa.

Daraktan fim din na ‘Makaranta’ ya musanta cewa wasu ne suke daukar nauyin sa, domin ya bata tarbiyyar mutane.

guardian newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Na yafe wa Buhari duk abun da ya yi min – Buba Galadima

Buba Galadima, wanda tsohon abokin marigayi Muhammadu Buhari ne...

Shugabannin Afrika za su halarci jana’izar Buhari

Ana sa ran wasu daga cikin shugabannin ƙasashen Afirka...

Yadda ake shirye-shiryen jana’izar Buhari a Daura

A yanzu haka dai alumma na ta tururuwa domin...

Shettima ya yi wa iyalan marigayi Muhammadu Buhari ta’aziyya a Landan

Mataimakin shugaban Najeriya Kashim Shettima ya yi wa wasu...

Indiya na jimamin mutuwar Buhari – Modi

Firaministan India Narendra Modi, ya shiga jerin shugabanni da...

Kungiyar Gwamnoni sun bayar da hutu kan mutuwar Buhari

Ƙungiyar gwamnonin arewa maso yammacin Najeriya sun bayyana kaɗuwarsu...

Tinubu ya bayar da hutu don yin ta’azziyar Buhari

Gwamnatin tarayya ta ayyana gobe Talata, 15 ga watan...

Shettima ya isa Landan domin dawo da gawar marigayi Muhammadu Buhari

A safiyar yau Litinin ne mataimakin shugaban Najeriya Kashim...

Najeriya ta yi rashin Buhari – Obasanjo

Tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo, ya bayyana rasuwar tsohon...

Tabbas Buhari mutum ne mai kyakyawan halaye mai kishin kasa – IBB

Tsohon shugaban mulkin soji a Najeriya, Janar Ibrahim Babangida,...

Tabbas Buhari dan kishin kasa ne – Tinubu

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya bayyana tsohon Shugaban Ƙasa,...

Najeriya ta yi rashin Dattijo – Atiku Abubakar

Tsohon Mataimakin Shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya bayyana Muhammadu...
X whatsapp