fidelitybank

Da Dumi-Dumi: Buhari ya umarci sojoji su murkushe ‘yan ta’adda Neja

Date:

Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya bukaci sojoji da su mayar da martani mai karfin gaske kan lamarin kashe-kashe da garkuwa da mutane a jihar Neja tare da tabbatar da dabarun da aka sa a gaba ta hanyar amfani da karfi.

Babban mataimaki na musamman ga shugaban kasa kan harkokin yada labarai, Garba Shehu ne ya tabbatar da hakan a ranar Lahadi, ya ce, shugaban ya bayar da umarnin ne ga shelkwatar tsaro.

Ya ce”shugaba Buhari a matsayinsa na babban kwamandan sojojin kasar nan ya shirya wani gagarumin farmakin soji a jihar Neja wanda ya ci gaba da fuskantar hare-haren ‘yan bindiga da ragowar ‘yan ta’addan Boko Haram a yankunan Arewa maso Yamma da Arewa maso Gabashin kasar nan”.

A sakonsa ga gwamnati da al’ummar jihar Neja, shugaba Buhari ya ce, “Ina so in mika sakon ta’aziyya ga gwamnati da al’ummar jihar, sakamakon matsalolin tsaro da suka faru a baya-bayan nan. Tsaro hakki ne na kowane memba na al’umma kuma ta hanyar hadin kai da hadin gwiwa da hukumomin tabbatar da doka, zamu iya shawo kan matsalolin a karshe”.

“Gwamnatin tarayya a shirye take ta karfafa goyon baya da hadin gwiwa da dukkan jihohin. Na yi imanin cewa tare da cikakken hadin kan ‘yan kasa, tabbas za mu shawo kan wannan matsala,” in ji shugaban kasar a cikin sanarwar mai taken “Big military Operation in Niger”.

A ranar Talatar da ta gabata ne ‘yan ta’adda suka mamaye al’umomin karamar hukumar Shiroro ta Neja, inda suka kashe mutane akalla 13 a wani harin da suka kai da rana a Nakundna da Wurukuchi.

Harin na ranar Talata ya zo ne kasa da makwanni biyu bayan wasu ‘yan bindiga sun kai hari kan ma’aikata a madatsar ruwan Zungeru, inda suka kashe mutane biyu tare da yin garkuwa da wasu ‘yan kasar China uku.

latest news in nigeria today 2022 punch

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mun ceto tsohuwa ƴar shekaru 80 daga masu garkuwa – Ƴansanda

Rundunar ƴansandan jihar Jigawa, ta ce ta ceto wata...

APC na taron kasu ruwa da tsaki

Jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya za ta gudanar da...

Matatar Ɗangote ta sake karya farashin fetur

Kamfanin Dangote da ya mallaki matatar mai ta Dangote...

Idan Isra’ila ta kai mana hari Amurka ce – Iran

Ministan harkokin wajen ƙasar Iran ya ce, gwamnatin Tehran...

Kotu ta daure mai kiwon Akuya bayan ta cinye shukokin gwamnatin Kano

Wata kotun majistare da ke Kano ta daure wasu...

‘Yansanda sun dakile yi garkuwa da mutane a Katsina

Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina ta dakile wani yunkurin...

‘Yansanda sun dakume ‘Yan Fashi uku a Kano

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta kama wasu ‘yan...

Jarumar Nollywood ta zama sojan ruwar Amurka

Fitacciyar jarumar nan ta Najeriya Grace Bassey wacce a...

Na yi takaicin barin Ancelloti daga Real Madrid – Carvajal

Dan wasan baya na kungiyar kwallon kafa ta Real...

Mu na shirin yin kawancen jam’iyya – PDP

Majalisar dattawa ta jam'iyyar PDP, ta bayyana shirin jam'iyyar...

Ana zanga-zanga a Binuwai sakamakon harbe Dalibi dan shekara 23

Wata zanga-zanga ta barke a Makurdi, babban birnin jihar...

A na cigaba da farautar Fursunonin Osun da suka tsere

Hukumar gyaran hali ta Najeriya (NCoS) ta ce, ta...
X whatsapp