Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya bukaci sojoji da su mayar da martani mai karfin gaske kan lamarin kashe-kashe da garkuwa da mutane a jihar Neja tare da tabbatar da dabarun da aka sa a gaba ta hanyar amfani da karfi.
Babban mataimaki na musamman ga shugaban kasa kan harkokin yada labarai, Garba Shehu ne ya tabbatar da hakan a ranar Lahadi, ya ce, shugaban ya bayar da umarnin ne ga shelkwatar tsaro.
Ya ce”shugaba Buhari a matsayinsa na babban kwamandan sojojin kasar nan ya shirya wani gagarumin farmakin soji a jihar Neja wanda ya ci gaba da fuskantar hare-haren ‘yan bindiga da ragowar ‘yan ta’addan Boko Haram a yankunan Arewa maso Yamma da Arewa maso Gabashin kasar nan”.
A sakonsa ga gwamnati da al’ummar jihar Neja, shugaba Buhari ya ce, “Ina so in mika sakon ta’aziyya ga gwamnati da al’ummar jihar, sakamakon matsalolin tsaro da suka faru a baya-bayan nan. Tsaro hakki ne na kowane memba na al’umma kuma ta hanyar hadin kai da hadin gwiwa da hukumomin tabbatar da doka, zamu iya shawo kan matsalolin a karshe”.
“Gwamnatin tarayya a shirye take ta karfafa goyon baya da hadin gwiwa da dukkan jihohin. Na yi imanin cewa tare da cikakken hadin kan ‘yan kasa, tabbas za mu shawo kan wannan matsala,” in ji shugaban kasar a cikin sanarwar mai taken “Big military Operation in Niger”.
A ranar Talatar da ta gabata ne ‘yan ta’adda suka mamaye al’umomin karamar hukumar Shiroro ta Neja, inda suka kashe mutane akalla 13 a wani harin da suka kai da rana a Nakundna da Wurukuchi.
Harin na ranar Talata ya zo ne kasa da makwanni biyu bayan wasu ‘yan bindiga sun kai hari kan ma’aikata a madatsar ruwan Zungeru, inda suka kashe mutane biyu tare da yin garkuwa da wasu ‘yan kasar China uku.