fidelitybank

Kano ta fi kowace jiha yawan almajiari – Ganduje

Date:

Gwamnan jihar Kano, Dr. Abdullahi Umar Ganduje ,ya bayyana cewa jihar ce ta fi kowace jiha yawan Almajirai a kasar nan.

Da ya ke magana da manema labarai yayin ganawa da manema labarai a fadar shugaban kasa dake Abuja, gwamnan ya koka da cewa, yawancin Almajirai ba ’yan asalin jihar ba ne.

Ya ce,“Eh, mu ne mafi yawan yaran Almajirai a Najeriya. Amma bari in gaya muku, mun dauki kididdiga. Yawancin wadannan Almajirai ba ’yan asalin jihar Kano ba ne, kuma a matsayinsu na ’yan Najeriya, suna da ’yancin zama a duk inda suke a kasar nan.

“Amma abin da ke da muhimmanci, mun bullo da ilimin firamare da sakandare kyauta, kuma wajibi a jihar Kano. Mun gina makarantun Islamiyya da dama. Mun gyara tsarin karatun Almajiri. Haka kuma, mun fara mayar da Almajiri zuwa jihohinsu, wasu har zuwa Jamhuriyar Nijar da Jamhuriyar Kamaru”.

“Domin haka kokarin da mu ke yi kenan. Amma kamar yadda na fada muku, matukar ba a samu hadin kai ba, musamman a tsakanin gwamnonin jihohin Arewa, inda aka yi dokar hana Almajiri daga wannan jiha zuwa wata jiha, Kano za ta ci gaba da fama da wannan matsalar.” In ji Ganduje.

vanguard 
nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...
X whatsapp