Hukumar yaki da cututtuka masu yaduwa ta kasa (NCDC) ta tabbatar da mutuwar mutane 80 wanda su ka kamu da cutar Zazzabin Lassa.
Hukumar ta tabbatar da hakan ne a taronta na bayar da rahoto kan barkewar cutar a Abuja, yayin ganawa da manema labarai.
Kawo yanzu an samu mutum 434 da su ka kamu da cutar a fadin Najeriya.
NCDC ta ce, daga watan Janairun 2021 zuwa yanzu, mutum 434 sun kamu da cutar, sannan mutum 80 sun mutu daga jihohi 17 da kananan hukumomi 63 da ke Najeriya,
Ta kuma ce, wannan cutar a Najeriya kamar sauran kasashe ta fi bayyana ne a lokacin sanyi, kamar daga watan Nuwamba zuwa watan Mayu a duk shekara.
Hukumar ta bayyana cewa, Jihar Edo na da mutum 192, Ondo 150, Taraba 21, Ebonyi 17, Bauchi 15, sai Benuwai mutum 8.
Filato na da mutum 8, yayin da Kaduna ke dauke da mutum 7 da su ka kamu.
Sauran jihohin sun hadar sa Enugu da mutum 5, Nasarawa na da 3, Kogi na da 3, Cross River na da mutum 1, Imo na da mutum 1, Anambra na da mutum 1, Delta na da mutum 1, sai jihar Abiya mai mutum 1.