fidelitybank

Ba ruwan Kannywood da sabon fim din da ya yamutsa hazo a Kano – Kwalle

Date:

Shugaban kungiyar masana’antar Kanywood, Alhassan Kwalle, ya barranta masana’antar su a kan wani shirin fim da a yanzu haka a ke tallansa a shafin YouTube.

Alhassan Kwalle ya bayyana hakan ne yayin wata ganawa da ya yi da manema labarai a kan sabon fim din da a ka far ace-ce-kuce a kan sa.

Alhassan Kwalle ya ce,”Shirin ya sabawa koyarwa ta addinin Musulci da al’adun Hausawa da kuma dokokin masana’antar, domin haka mun barranta kan mu da fim din. Kuma za mu tabbatar da cewa za mu dauki matakan da ya dace na shari’a a kan wanda ya shirya fim din ,duk da mashiryin shirin ba dAn masana’antar mu ba ne.

“Mun yi waya da mashiryin shirin, domin in sanar da shi cewa abun ba dai-dai bane, Amma tun farko ya ce shi fa ba dan Kanywood ba ne, ya shirya shirin ne a karan kansa. Ina da yakinin hukumar tace fina-finan ta jihar Kano ba za ta bar abun sakakaba, yasan za ta dauki matakin da ya dace, domin hana fitar da fim din gudun lalata tarbiyyar al’umma”. Inji Alhassan.

A Jawabinsa shugaban hukumar tace fina-finan Hausa da Dab’I ta Jihar Kano, Isma’ila Na-Abba afakallah, ya ce, ba za mu lamunci irin badalar cikin fina-finan ba, ina da tabbacin hukumar mu za ta nemi mashiryin shirin fim din, domin gurfanar da shi a gaban shari’a. Aikin hukumar ne ta ha na yin fim din da ya sabawa addinin Musulci da al’adun Malam Bahaushe, domin tabbatar da sauke nauyin da Gwamnati ta dora wa hukumar.

Shirin fim din mai suna Makaranta ya dai yamutsa hazo tun bayan sakin tallan kadan daga cikin wani bangaren sa a shafin Youtube.

 

world news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...
X whatsapp