fidelitybank

Ba ruwan Kannywood da sabon fim din da ya yamutsa hazo a Kano – Kwalle

Date:

Shugaban kungiyar masana’antar Kanywood, Alhassan Kwalle, ya barranta masana’antar su a kan wani shirin fim da a yanzu haka a ke tallansa a shafin YouTube.

Alhassan Kwalle ya bayyana hakan ne yayin wata ganawa da ya yi da manema labarai a kan sabon fim din da a ka far ace-ce-kuce a kan sa.

Alhassan Kwalle ya ce,”Shirin ya sabawa koyarwa ta addinin Musulci da al’adun Hausawa da kuma dokokin masana’antar, domin haka mun barranta kan mu da fim din. Kuma za mu tabbatar da cewa za mu dauki matakan da ya dace na shari’a a kan wanda ya shirya fim din ,duk da mashiryin shirin ba dAn masana’antar mu ba ne.

“Mun yi waya da mashiryin shirin, domin in sanar da shi cewa abun ba dai-dai bane, Amma tun farko ya ce shi fa ba dan Kanywood ba ne, ya shirya shirin ne a karan kansa. Ina da yakinin hukumar tace fina-finan ta jihar Kano ba za ta bar abun sakakaba, yasan za ta dauki matakin da ya dace, domin hana fitar da fim din gudun lalata tarbiyyar al’umma”. Inji Alhassan.

A Jawabinsa shugaban hukumar tace fina-finan Hausa da Dab’I ta Jihar Kano, Isma’ila Na-Abba afakallah, ya ce, ba za mu lamunci irin badalar cikin fina-finan ba, ina da tabbacin hukumar mu za ta nemi mashiryin shirin fim din, domin gurfanar da shi a gaban shari’a. Aikin hukumar ne ta ha na yin fim din da ya sabawa addinin Musulci da al’adun Malam Bahaushe, domin tabbatar da sauke nauyin da Gwamnati ta dora wa hukumar.

Shirin fim din mai suna Makaranta ya dai yamutsa hazo tun bayan sakin tallan kadan daga cikin wani bangaren sa a shafin Youtube.

 

legit news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp