An sallami shugaban kasar Brazil, Jair Bolsonaro daga asibiti a ranar Laraba, kwanaki biyu bayan an kwantar da shi sakamakon toshewar hanji.
Tun a shekarar 2018 lokacin gangamin yakin zaben san a shugaban kasar, wni ya caka masa wuka a ciki, lamarin da ya rinka haifar masa da ciwon ciki.
Bolsonaro ya shaida cewa, “An sallame ni yanzu. Na gode duka, “shugaban na Brazil mai ra’ayin mazan jiya ya wallafa a shafin Twitter.
Likitan Bolsonaro, Antonio Macedo, ya shaida wa manema labarai cewa, shugaban ya murmure kuma a shirye ya ke ya koma bakin aiki, ya kara da cewa zai kasance kan abinci na musamman, sannan a karshen mako kuma ba zai iya yin ayyukan motsa jiki ba, har sai ya murmure.
Bolsonaro, wanda ke kan karagar mulki tun shekarar 2019, kuma ya na shirin sake tsayawa takara a zaben shugaban kasa da aka shirya yi a watan Oktoba, ya ce zai ci gaba da gudanar da manufofin saa na yau da kullum, ciki har da ziyarar da zai kai kasar Rasha a watan Fabrairu.
A yanzu haka Bolsonaro na hutu ne a jihar Santa Catarina da ke Kudancin Brazil lokacin da a ka kai shi cikin gaggawa zuwa asibitin na Vila Nova Star da ke Sao Paulo da sanyin safiyar Litinin bayan fama da ciwon ciki.