fidelitybank

An tsige shugaban kwamitin tsaro a Kazakhstan a kan zanga-zanga man fetur

Date:

Shugaban kasar Kazakhstan ya tube guda daga cikin kusa a tafiyar sa a harkokin tsaron kasar daga mukaminsa na shugaban majalisar tsaron kasar a ranar Laraba, bayan da masu zanga-zangar suka kutsa kai tare da kona gine-ginen jama’a a wani rikici mafi muni da kasar ta shafe fiye da shekaru goma ana yi.

Majalisar ministocin ta yi murabus, amma hakan ya gaza kwantar da hankulan masu zanga-zangar bayan kwashe tsawon kwanaki a na tashe tashen hankula, sakamakon tashin farashin mai a kasar da ke hako mai a tsakiyar yankin Asiya.

Wasu masu zanga-zangar sun yi ta rera taken adawa da Nursultan Nazarbayev, mai shekaru 81, wanda ya ci gaba da rike madafun iko tun bayan da ya sauka a shekarar 2019 a matsayin wanda ya fi dadewa kan karagar mulki a tsohuwar kasar ta Soviet.

Wanda ya gaji Nazarbayev, shi ne shugaba, Kassym-Jomart Tokayev, ya ce, ya karbi ragamar jagorancin kwamitin tsaro mai karfi mukamin da Nazarbayev ya rike.

Har yanzu dai a na kallon tsohon shugaban a matsayin babban jigon siyasa a Nur-Sultan, babban birnin da a ka gina da sunan sa. An yi imanin danginsa suna sarrafa yawancin tattalin arzikin kasar.

 

news today in nigeria 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama Æ´an Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na Æ™asa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta É—aure Matashin da ya shiga É—akin kwanan ÆŠalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaÆ™i don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin Æ™era nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe Æ´an Æ™asarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faÉ—a kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta Æ™addamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo Æ™arshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar Æ´ansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...
X whatsapp