Majalisar dokokin ta tarraya ta yi wa kudurin dokar zabe gyaran fuska, ta yadda a yanzu ‘yan majalisun suka baiwa jam’iyyun siyasa damar zaben tsarin da suke so wajen fitar da ‘yan takara.
Gyaran da majalisun biyu ta dattawa da kuma ta wakilai suka yi, a yanzu kudurin ya tanadi kowace jam’iyya cewa za ta iya fitar da ‘yan takararta ta hanyar zaben ‘yar tinke ko kai tsaye ko kuma ta sasanci.
Majalisun sun zartar da cewa kowace jam’iyya za ta rinka fitar da ‘yan takararta ne ta hanyar zaben ‘yar tinke kawai.
Bayan an mika wa shugaba, Muhammadu Buhari, ya sanya hanu a kan kudurin, domin ya zama doka sai ya ki amincewa da wannan tsari, ya na bukatar su bayar da wani zabi, abin da ya sa aka mayar wa hadakar majalisar kudurin, domin ta sake bibiyar kudurin tare da yin kwaskwarimar.
A yayin zaman da suka yi ne daban-daban a ranar Larabar nan, aka sake gabatar da kudurin, wanda Sanata Yahaya Abdullahi ya gabatar da shi a majalisar dattawa yayin da Abubakar Fulata ya gabatar a majalisar wakilai. A cewar BBC.