Mai dakin gwamnan jihar Kano, Farfesa Hafsat Abdullahi Umar Ganduje, ta sha alwashin tsayawa wajen tabbatar da an kwatowa Hanifa Abubakar hakkinta a wajen malamin su Abdulmalik Tanko wanda ya yi garkuwa da ita ya kuma kashe ta.
Farfesa Hafsat na wannan jawabin ne lokacin da ta kai ziyarar ta’aziya wajen iyayen Hanifa a yau Laraba.
Mai dakin gwamnan ta sami rakiyar shugaban karamar hukumar Nasarawa, Auwalu Shu’aibu Aranposu, da shugabar Mata ta jam’iyyar APC, Hajiya Fatima Abdullahi Dala da Ma’ajin Jam’iyyar, Hajiya Yardada MaiKano Bichi da sauran masu baiwa gwamna shawara fanni daban-daban na jihar Kano.