fidelitybank

Iyayen wanda ya kashe Hanifa sun tsere daga unguwar su gudun kai musu farmaki

Date:

Iyayen wanda ya kashe ‘yar shekara 5, Hanifa Abubakar; Abdulmalik Tanko, sun tsere daga gidansu saboda fargabar kai musu hari.

Politics Nigeria ta rawaito cewa, gidan dangin Tanko ya na a unguwar Tudunwada da Tudun Murtala a jihar Kano. Har yanzu ba a san inda iyayensa suke ba.

An fahimci cewa, sakamakon wannan danyen aikin na Tanko, an yi yunkurin kai wa iyayen sa hari. Wannan ci gaban ya sa iyayen mai laifin su ka gudu daga gidansu.

Tanko, mamallakin makarantar Noble Kids da ke Kano da aka kama bisa kisan Hanifa ya ce, ya kashe ta ne da maganin Bera.

Malamin makarantar wanda ‘yan sanda suka kama shi a ranar Alhamis din da ta gabata, ya amsa laifinsa ne a lokacin da yake amsa tambayoyi kan hannu a cikin wannan aika-aika.

A cewarsa, makarantar tana da rassa biyu kuma na farko  inda aka binne Hanifa  an bude ta a shekarar 2017.

Da yake bayar da cikakken bayani kan lamarin, Tanko ya ce ya tuntubi abokinsa mai suna Hashimu Isyaku da kuma wata Fatima Musa domin su yi garkuwa da yarinyar da farko amma suka kasa aiwatar da garkuwar.

Ya ce daga cikin Naira miliyan 6 da ake nema a matsayin kudin fansa, ya karbi Naira 100,000 kafin a kashe Hanifa, inda ya ce “Na yi amfani da Naira 71,000 wajen biyan ma’aikatan wani reshen.

Labarin dai ya janyo ce-ce-ku-ce a shafukan sada zumunta, inda da dama ke neman a yi musu adalci ba tare da bata lokaci ba.

sun newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...
X whatsapp