Sanata mai wakiltar Kano ta tsakiya, Malam Ibrahim Shekarau, ya sha alwashin da kan sa zai ci gaba da bin diddigin zargin kisan gillar da aka yi wa Hanifa mai shekara biyar da malaminta Abdulmalik Tanko ya kashe.
A wani sako da ya aikewa ‘yan uwa, Sanata Shekarau, ya ce zai bi diddigin lamarin, domin ganin an yi adalci.
Tun dai a ranar 4 ga watan Disambar bara ne dai mai makarantar su, Abdulmalik Tanko, ya sace Hanifa Abubakar, yayin da ta ke dawowa daga Islamiyya.
Sai dai bayan ya bukaci iyalanta a biya su kudin fansa Naira miliyan 6, inda aka bashi Naira 100,000, daga bisani ya kashe yarinyar mai shekaru 5 da maganin Bera na Naira 100.
Haka zalika a daren jiya Lahadi ne, wasu matasa da ba a san ko su wanene ba, suka kona makarantar su Hanifa Nobles Kids Academy.