fidelitybank

Zamu ci gaba da samar da tsaro a Kano – Laftanar Janar Farouk

Date:

Babban hafsan sojin kasa, Laftanar Janar Farouk Yahaya, ya yi alkawarin cewa, sojojin Najeriya za su yi nasara a kan dukkan kalubalen tsaro da ke barazana ga ci gaban zamantakewa da tattalin arzikin kasar.

Yayin da yake kaddamar da rukunin masauki da kuma hulda da sojoji a bataliya ta 73 dake Barikin Janguza dake Kano, Laftanar Janar Yahaya, ya bayyana cewa, ya ziyarci kusan daukacin rundunonin sojoji a sassa daban-daban na kasar nan, ya na mai jaddada cewa, sojojin na samun nasara a yakin da suke yi a kan masu tayar da kayar baya a dukkan sassan kasar.

“Na yi mu’amala da sojojin, na yaba musu, domin ci gaba da yin iya kokarinsu. Kuma da jajircewarsu, na ji dadin lura cewa, za mu ci gaba da cimma burinmu. Kuma tare da hadin kan masu ruwa da tsaki, za mu dakile barazanar da ke barazana ga kasarmu.

“Za mu ci gaba da tallafawa sojojin, kuma shi ya sa muka zo nan domin magance wasu batutuwan da ke faruwa a kasa, musamman wurin kwana. Mun ba da umarni matakai da yawa na masauki. Kuma ba mu jajirce ba, za mu ci gaba da goyon bayan da muke samu daga shugaban kasa. 

“Muna kan gaba kuma ba za mu yi kasa a gwiwa ba. Kuma tare da sauran hukumomi, za mu yi nasara kan wadannan barazanar,” in ji shugaban rundunar.

Sai dai Gwamna Ganduje ya bayyana bukatar hadin gwiwa tsakanin Sojoji da Sojojin Sama na Najeriya, ‘Yan Sanda, DSS da sauran jami’an tsaro, kamar hukumar kwastam, NDLEA, da dai sauran su wajen yaki da kalubalen tsaro.

legit

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naɗa shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...

‘Yar Najeriya ta haihuwa a aikin Hajjin bana

Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar...

Rashin nadi da jinkiri ne ya kawo rashin nasarar mu a kakar 2024/2025 – Kano Pillars

Kungiyar Kano Pillars ta yi imanin cewa jinkirin shirye-shiryen...
X whatsapp