fidelitybank

Safarar mutane: Kotu ta yankewa dan kasar Kamaru hukunci a Kano

Date:

Wata babbar kotun tarayya a Kano, ta yankewa wani dan kasar Kamaru, Wamba Jean-Gaston mai shekaru 41, hukuncin daurin shekaru biyar a gidan gyaran hali, bisa samunsa da laifin safarar wasu matasa mata uku da maza hudu daga kasar Kamaru zuwa Najeriya daga nan kuma ya wuce da su Turai.

Matan uku da abin ya shafa su ne: Belinga Ovanda mai shekaru 19 da Koussene Agnes, mai shekaru 21 da Meye Uwono mai shekaru 27 yayin da mazan su ne Thomas Ange, mai shekaru 21 da Ovanda Rodrigue, mai shekaru 21 da Boris Kouass, mai shekaru 20 tare da Yannick Poudjom, mai shekaru 18.

Mai shari’a Abdullahi Muhammed-Liman ya yankewa Jean-Gaston hukunci, bayan ya amsa laifuka biyu da ake tuhumarsa da shi.

Liman ya bayyana damuwarsa kan tasirin da mai laifin ke da shi ga rashin tsaro a yankin baki daya da ya shafi kasashe da dama.

Tun da farko, Lauyan hukumar hana safarar mutane ta kasa (NAPTIP), Mista Abdullahi Babale, ya shaidawa kotu cewa, an kama wanda ake tuhuma a Kano ranar 10 ga watan Disamba, 2021.

Babale ya ce, an kama dan Kamarun ne tare da mutanen bakwai da aka kashe a kan hanyarsu ta zuwa kasar Aljeriya.

Ya ce, mai laifin ya na sarrafa takardun shiga ba bisa ka’ida ba ga wadanda aka yi safarar su zuwa kasashen Algeria da Turai ta Najeriya da Jamhuriyar Nijar, ba tare da takardar izinin zama ko biza ba.

Lauyan ya ce, laifin ya sabawa sashe na 26 (1) na dokar tilastawa mutane fataucin mutane, 2015.

nnn.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama Æ´an Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na Æ™asa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta É—aure Matashin da ya shiga É—akin kwanan ÆŠalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaÆ™i don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin Æ™era nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe Æ´an Æ™asarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faÉ—a kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta Æ™addamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo Æ™arshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar Æ´ansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...
X whatsapp