Rundunar ƴan sandan jihar Zamfara ta ceto ƙananan yara 21, ciki har da mata biyu waɗanda ke hanyarsu ta zuwa wata makarantar Islamiyya ta Almajirai da ke Katsina.
A wata sanarwa da mai magana da yawun ƴan sandan jihar Zamfara, SP Mohammed Shehu ya fitar, sanarwar ta ce, yaran sun taso ne daga ƙauyen Rini da ke Ƙaramar Hukumar Bakura ta jihar Zamfara.
Tun da farko jami’an tsaron sun samu labarin cewa, ƴan bindiga sun tare hanyar Gusau zuwa Funtua ta ɓangaren Kucheri, inda su ka yi garkuwa da mutanen da ba a san adadinsu ba daga motoci biyar. Hakan ya sa jami’an suka nufi wurin inda su ka yi bata-kashi da ƴan bindigan.
Ƴan sandan Zamfaran dai sun yi kira ga musamman direbobi da fasinjoji da su kiyayi tafiyar dare, inda su ka ce akasari da dare ne ɓarayi ke tare hanya.