Mai martaba Sarkin Bichi, Alhaji Nasiru Ado Bayero, ya umarci al’ummar masarautar Bichi da su gudanar da addu’o’I na musamman a ranar juma’a mai zuwa, domin neman tabbatuwar da zaman lafiya a Najeriya.
Cikin wata sanarwa da a ka rabawa manema labarai mai dauke da sa hannun sakataren masarautar, Abubakar Ibrahim Yakasai, ya ce babban abinda ya ja hankalin masarautar shi ne kisan da a ka yi wa wasu al’ummar Sokoto a baya bayan nan.
Alhaji Nasiru Ado Bayero ya kuma bayyana damuwar sa matuka, a kan yadda a ke kashe wadanda ba su ji ba ba su gani ba, domin haka sarkin ya bukaci al’ummar kasar Bichi da su gabatar da addu’oin na musamman a ranar juma’a mai zuwa.