fidelitybank

YANZU-YANZU: Gwamnatin Kano ta rufe makarantar da a ka binne Hanifah 

Date:

 

Gwamnatin Nijar Kano ta bada umarnin rufe Noble Kids Academy, makarantar kuɗi da ke Kwanar Dakata, inda a nan ne Abdulmalik Tanko, wanda ya yi garkuwa da Hanifah Abubakar, ƴar shekara 5, ya kashe ya kuma binne ta.
Daily Nigerian Hausa ta rawaito cewa a jiya da daddare ne dai dubun Tanko ta cika, wanda shine malamin Hanifah a makarantar, amma ya sace ta ya kuma hallaka ta bayan ya karɓi wani kaso na naira miliyan 6 da ya nema a matsayin kuɗin fansa.
Da ya ke sanar da rufe makarantar na gaggawa a yau Alhamis, Kwamishinan Ilimi na Jihar Kano, Muhammad Sa’idu Ƙiru, ya ce za a rufe makarantar ne bayan ƴan sanda sun gano gawar yarinyar a makarantar.
Da ya ke nuna takaici a kan lamarin a wata sanarwa da ya fitar, Ƙiru ya ce gwamnati za ta fara tantance makarantu mau zaman kan su domin a fito da wadanda basu da rijista domin magance aiyukan ɓatagari.
Ya kuma yi kira ga iyayen daliban makarantar Noble Kids Academy din da su tsaya da kai ya’yan su har sai an kammala bincike.

ng news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp