fidelitybank

YANZU-YANZU: An samu mutum 2 ɗauke da sabon nau’in Omicron na korona

Date:

 

 

Cibiyar Kula da Cututtuka ta Ƙasa, NCDC ta tabbatar da samun sabon nau’in korona mai suna Omicron.

A wata sanarwa da Darakta-Janar na NCDC, Ifedayo Adetifa ya sanyawa hannu a yau Laraba, cibiya ce ta gano nau’in cutar ne mai haɗari a wani gwaji da ta yi.

Ta ƙara da cewa ana zargin waɗanda a ka gwada samfurin nasu sun taho ne daga ƙasar Afirka ta Kudu, inda a nan ne nau’in ya samo asali.

Cibiyar ta ƙara da cewa ta gano sabon nau’in koronan ne a gwaje-gwajen da ta ke yi na matafiya domin daƙile yaɗuwar cutar.

NCDC ta kuma baiyana cewa mutane biyun da a ka samu da sabon nau’in cutar ba su nuna wata alama ta rashin lafiya ba, inda ta ƙara da cewa an fara bibiyar mutanen da su ka yi mu’amala da su.

breaking news in nigeria today punch

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...
X whatsapp