fidelitybank

‘Yan sandan Zamfara sun kama matar da take kokarin siyar da dan kishiyarta

Date:

Rundunar ƴan sandan Jihar Zamfara ta kama wata mata da ake zargi da yunƙurin sayar da yaro ɗan shekara biyu.

Jaridar Punch ta rawaito cewa, kwamishinan ƴan sanda na jihar, Ayuba Elkana ya ce, an kama matar ne tun a ranar 8 ga watan Janairu a yankin Tullukawa da ke Gusau inda ake zargin matar da yunƙurin sayar da ɗan kishiyarta.

Matar wadda asalinta mutumiyar ƙauyen Danyade ce, da ke Maradi a Jamhuriyyar Nijar, an kama ta ne ɗauke da ɗan kishiyarta wadda ta shaida wa jami’an tsaro cewa, ta sato yaron ne daga wajen kishiyarta, domin ita ma ta rama sata da sayar da ɗanta da kishiyarta ta yi a baya.

Amma daga baya ta ƙara shaida wa jami’an tsaro cewa, ta yi yunƙurin sayar da yaron ne, domin samun kuɗin biyan buƙatunta na yau da kullum.

Rundunar ƴan sandan ta ce, za a miƙa wadda ake zargi zuwa ga hukumar kula da shige da fice ta Najeriya domin zurfafa bincike.

natforce latest news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...
X whatsapp