fidelitybank

‘Yan sanda sun kama mutumin da ya kashe dalibar jami’ar Jos

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Filato, ta gurfanar da Moses Okoh, mai shekaru 20, wanda a ke zargin ya kashe Jennifer Anthony, daliba mai matakin ajin level 300 na Jami’ar Jos (UNIJOS), wadda a ka tsinci gawarta a ranar 1 ga watan Janairu, a wani gidan baki a Jos.

Okoh wanda a ke zargin saurayinta ne ya gudu, bayan ya aikata laifin. Sabon kwamishinan ‘yan sandan jihar Filato, Bartholomew Nnamdi Onyeka, a cikin jawabinsa na farko ga manema labarai, ya gabatar da wanda a ke zargin da sauran masu aikata laifuka, inda ya haddasa barna, kashe-kashe da kuma yin garkuwa da mutane a jihar.

CP ya bayyana cewa, rundunar ‘yan sandan a yunkurinta na cafke Okoh, ta kaddamar da farautarsa tare da bibiyar shi da dabara zuwa jihar Benuwe inda ‘yan sanda su ka kama shi.

Ya ce”Za a gurfanar da wanda a ke zargin a gaban kotu da zarar an kammala bincike”.

Wanda a ke zargin an daure shi a bayansa da duk wani farin kyalle mai cike da jini wanda a ka yi amfani da shi wajen fizge idanuwa Jennifer, magunguna da kayan da a ka yi amfani da su wajen gudanar da aikin sa a yayin holonsa.

legitnewsnigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

QPC ta nemi INEC ta soke zaɓen Kano

Jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya ta nemi hukumar zaɓe...

Zaɓen Kano: An kama Mutane 288 da tayar da zaune tsaye

Rudunar ƴansandan jihar Kano, ta sanar da kama mutum...

An Kama wakilin jam’iyya da Naira miliyan 25.9 na Siyan Kuri’a

Jami’an tsaro sun kama wani da ake zargin wakilin...

Farashin kayan abinci na rugu-rugu a Najeriya – NBS

Hukumar Ƙididdiga ta Ƙasa (NBS) ta ce hauhawar farashin...

Kotun Kano ta ce a kamo mata Dagacin Tamburawa

Kotun Shari’ar Musulunci da ke shelkwatar Hisbah a Kano,...

Kotu ta ƙwace motocin gwamnatin Zamfara guda 40 daga hannun Matawalle

Kotun Daukaka Kara da ke a Sokoto ta tabbatar...

A na cigaba da gudanar da zaben cike gurbi harda Kano

Kano na ɗaya daga cikin jhihohin da ake kaɗa...

Mutane 12 sun mutu a wani hatsari a Kano – FRSC

Hukumar Kiyaye Haddura ta Ƙasa (FRSC) reshen Kano, ta...

Masarutar Rano ta haramta aurar da Yaran da ba su kammala karatun Firamare ba

Masarautar Rano a Kano ta haramta cire yarinya daga...

Matatar Dangote za ta fara jigilar mai kyauta ga gidajen mai

Matatar man Dangote za ta fara jigilar mai kyauta...

An sassata rikicin da aka shafe shekaru 30 kan Masallacin Sharada da Islamiyya

Tsohon dan takarar gwamnan Kano, Malam Sha’aban Ibrahim Sharada,...

Duk da kalubalen ‘yan siyasa a Kano mun shirya a zaben cike gurbi – INEC

Kwamishinan hukumar zaɓe mai zaman kanta (INEC) reshen jihar...
X whatsapp