Rundunar ƴan sandan jihar Kaduna ta ceto mutum tara da a ka yi garkuwa da su tare da kama mutum biyu da a ke zargin ƴan bindiga ne inda kuma su ka kashe ɗaya.
Mai magana da yawun rundunar, Kaduna Mohammed Jalige ne ya sanar da hakan, inda ya ce, an samu wannan nasara ne bayan haɗin gwiwar jami’an tsaro da jami’an sa kai inda su ka kai samame ɗaya daga cikin sansanin ƴan bindigar da ke a dajin Sabon Birni na Karamar Hukumar Igabi a Jihar Kaduna.
Ya bayyana cewa an kai wannan samame ne bayan an samu bayanan sirri da ke cewa akwai waɗanda aka yi garkuwa da su aka ajiye su a cikin dajin.
Mutum Takwas cikin Tara sun koma ga iyalansu, bayan an duba lafiyarsu a asibitin ƴan sanda, sai dai akwai mutum guda da a ka tafi da shi wani asibitin koyarwa da ke jihar, sakamakon raunin da ya samu bayan harbinsa da a ka yi da bindiga.