fidelitybank

2023: Mu yi azumi da addu’a Allah ya kubutar da Najeriya – CAN

Date:

Kungiyar Kiristocin Najeriya CAN, ta shawarci shugabannin Najeriya da kada su yi watsi da kokarin da su ke yi na magance dimbin kalubalen da kasar ke fuskanta a yunkurinsu na son kai na samun mukamai a babban zabe mai zuwa na 2023.

A sakonta na sabuwar shekara ga ’yan Najeriya mai dauke da sa hannun shugaban CAN, Rabaran Samson Ayokunle, kungiyar ta bukaci kowa ya yi amfani da damar shiga sabuwar shekara, domin yin azumi da addu’o’i na rokon Allah ya kubutar da Nijeriya daga wadanda su ke da niyyar ruguza ta.

Kungiyar ta CAN ta koka da yadda ayyukan ‘yan fashi da ‘yan ta’adda, masu garkuwa da mutane da sauran abubuwan rashin gaskiya su ka sanya akasarin sassan Najeriya cikin rashin tsaro.

Ya ce,”Masu aikata laifuka sun mamaye kasar, sun mamaye al’ummomi, kasuwanni, coci-coci da makarantu suna kashewa, lalata da lalata dukiyoyi ba tare da tsangwama”. Inji Rabaran.

Kungiyar ta CAN ta kuma koka kan yadda a yanzu ya zama babban abin da ‘yan siyasa ke mayar da hankali a kai shi ne zaben 2023.

“2021 shekara daya ta yi yawa a sakamakon hanyoyi da dabi’u da wadannan miyagu ke gudanar da ayyukansu ba tare da hukunta su ba, kamar ba kasar nan ba ce da mu ka kasance a wadannan shekarun.

“Allah ne kadai zai iya tabbatar da zaben 2023 mai zuwa. Allah ne kawai a hanyarsa wanda zai iya koya wa shugabanninmu matakin da ya dace. Allah ne kadai zai iya aiko mana da taimako daga sama. Saboda halin da mu ke ciki, tuni wasu gwamnonin ke ta kiraye-kirayen a kare kansu da kuma ayyana dokar ta-baci! Wannan ba irinsa ba ne.

“Ina kira ga daukacin mabiya darikar mu da shuwagabannin cocin mu da su yi amfani da damar shirin azumi da addu’o’in sabuwar shekara na coci-cocin mu, domin kubutar da Nijeriya daga wadanda su ke da niyyar ruguza ta ta hanyar yin addu’a da gangan, domin neman rahamar Allah a kan halin da mu ke ciki. Gama Ubangiji Allah mu Allah ne mai jinƙai. Ba zai bar mu ba ko ya bar wadannan miyagu marasa zuciya su halaka mu,” in ji CAN.

www.nigeriannewspapers.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...
X whatsapp