Rundunar ƴan sandan kasar nan ta kama mutum huɗu cikin tara waɗanda ake zargi da kai hari shagon abincin wata matashiya da ke babban wajen wasan yara na Jihar Borno.
A cikin makon nan ne dai wani bidiyo ya rinƙa yawo a shafukan sada zumunta wanda ya nuna yadda wasu mutane suna zabga wa wata mari da kuma zaginta.
Wadda aka rinƙa duka a bidiyon mai suna Fadila Abdulrahman na da shagon sayar da abinci ne mai suna Zuhura Restaurant a Maiduguri, inda waɗanda suka ci mutuncin na ta suka rinƙa iƙirarin cewa, ta yi wa ɗan majalisa Ahmed Satomi butulci.
Sai dai Ahmed Satomi ya musanta batun, tare da cewa, ba shi da wata alaƙa da wadanda suka aikata wannan lamari.