Gwamnan jihar Ondo, Rotimi Akeredolu, ya bukaci ‘yan yankin Kudu maso Yamma da su daina cin naman Sa, sakamakon yankin na asarar Naira biliyan 2.5 a kullum.
Kungiyar masu fafutukar kafa kasar Biafra (IPOB) a kwanakin baya ta haramta cin naman Sa da kuma kiwon Shanu a yankin Kudu maso Gabas.
Da ya ke jawabi a wajen wani taro da masu ruwa da tsaki a fannin ilimi na jihar a Akure, babban birnin Ondo, Akeredolu, ya ce, ya kamata al’ummar yankin Kudu maso Yamma su yi la’akari da amfani da naman kaji wajen bukukuwan su.
Gwamnan wanda ya samu wakilcin mai ba shi shawara na musamman kan harkokin noma, Akin Olotu, ya ce, naman kaji ya fi naman Sa lafiya, kuma hakan zai bunkasa tattalin arzikin yankin.
“Shugaban ya ce ku shuka abin da ku ke ci ku ci abin da ku ka noma. Na kasance mai ba da shawara sosai kuma ina sake jaddada hakan, domin Allah mu yi amfani da Kaza wajen bukukuwan mu,” inji shi.