fidelitybank

‘Yan bindiga sun yi awon gaba da ‘yan kasuwar Kano da ba a tantance adadin su ba

Date:

Wasu ‘yan bindiga sun yi awon gaba da wasu ‘yan kasuwar Kano wadanda ba a tantance adadinsu ba, a kusa da dajin Ungwan Yako da ke karamar hukumar Birnin-Gwari ta jihar Kaduna a ranar Laraba.

Wata majiya ta bayyana cewa, ‘yan bindigar sun tare babbar hanyar ne a daidai lokacin da ‘yan kasuwar ke tafiya Kano daga Brinin Gwari inda a ke zargin su da kai wadanda harin ya rutsa da su zuwa wani wuri da ba a sani ba.

Hanyar Birin zuwa Gwari, a tsawon shekaru, ta zama tarkon mutuwa ga masu ababen hawa da matafiya, sakamakon munanan ayyukan ‘yan bindiga da su ka addabi hanyar, wadda ta kasance hanyar shiga yankin Kudu maso Yammacin kasar nan zuwa jihar Kaduna.

PUNCH ta rawaito cewa, wasu ‘yan bindiga sun kai hari kan ayarin motocin tare da yin awon gaba da ‘yan kasuwa sama da 70 daga Kano a kan hanyar Birnin Gwari zuwa Kaduna a ranar 22 ga Disamba, 2021.

Sai dai rundunar ‘yan sanda a Kaduna cikin kasa da sa’o’i 24, ta tattara tare da kubutar da 48 daga cikin wadanda lamarin ya shafa, yayin da wata mace da a ka kashe ba a san inda ta ke ba har zuwa yau.

Har yanzu dai ba a tabbatar da faruwar lamarin ba, ko dai daga gwamnatin jihar ko kuma rundunar ‘yan sandan jihar.

Har ya zuwa lokacin hada wannan rahoto, mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan jihar, ASP Mohammad Jalige, bai amsa kiransa ba ko kuma amsa sakon wayarsa.

Majiyar ta ce wadanda harin ya rutsa da su sun yi tattaki ne daga Birnin Gwari inda suka je Kano kafin masu garkuwar su tafi da su.

A cewarsa, wasu matafiya sun ga motocin da babu kowa a gefen hanya, inda ya kara da cewa maharan na shiga cikin dajin Yako mai firgita.

nnn news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko ƴanƙwallon...

Sunderland ta ɗauko ƴanƙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ƙwallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...

Luiz Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool

Luis Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool...

NNPCL ya musanta sayar da matatar mai ta Fatakwal

Babban kamfanin man fetur na kasa, NNPCL ya musanta...

Mun samu kuɗin gina titin jirgi daga Maiduguri zuwa Abia – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ce, ta samu duka kuɗin gudanar...

Sanatocin Arewa sun yi tir da kisan Zamfara

Ƙungiyar sanatocin Arewa, ta yi Allah wadai da kisan...

Tattalin arzikin Najeriya zai kara bunkasa a shekarar nan – IMF

Asusun Bayar da Lamuni na Duniya, IMF ya sabunta...

Ma’aikatan jinya sun fara yajin aiki a Najeriya

Ƙungiyar ma'aikatan jinya da unguzomomi ta kasa, ta fara...

Birtaniya ta na tsantsanr goyon bayam Hamas ne kawai – Netanyahu

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, matakin da Birntaniy...

Birtaniya ta gindaya wa Isra’ila sharuɗa

Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya shimfiɗa wa Isra'ila wasu...
X whatsapp