fidelitybank

‘Yan bindiga sun yi awon gaba da ‘yan kasuwar Kano da ba a tantance adadin su ba

Date:

Wasu ‘yan bindiga sun yi awon gaba da wasu ‘yan kasuwar Kano wadanda ba a tantance adadinsu ba, a kusa da dajin Ungwan Yako da ke karamar hukumar Birnin-Gwari ta jihar Kaduna a ranar Laraba.

Wata majiya ta bayyana cewa, ‘yan bindigar sun tare babbar hanyar ne a daidai lokacin da ‘yan kasuwar ke tafiya Kano daga Brinin Gwari inda a ke zargin su da kai wadanda harin ya rutsa da su zuwa wani wuri da ba a sani ba.

Hanyar Birin zuwa Gwari, a tsawon shekaru, ta zama tarkon mutuwa ga masu ababen hawa da matafiya, sakamakon munanan ayyukan ‘yan bindiga da su ka addabi hanyar, wadda ta kasance hanyar shiga yankin Kudu maso Yammacin kasar nan zuwa jihar Kaduna.

PUNCH ta rawaito cewa, wasu ‘yan bindiga sun kai hari kan ayarin motocin tare da yin awon gaba da ‘yan kasuwa sama da 70 daga Kano a kan hanyar Birnin Gwari zuwa Kaduna a ranar 22 ga Disamba, 2021.

Sai dai rundunar ‘yan sanda a Kaduna cikin kasa da sa’o’i 24, ta tattara tare da kubutar da 48 daga cikin wadanda lamarin ya shafa, yayin da wata mace da a ka kashe ba a san inda ta ke ba har zuwa yau.

Har yanzu dai ba a tabbatar da faruwar lamarin ba, ko dai daga gwamnatin jihar ko kuma rundunar ‘yan sandan jihar.

Har ya zuwa lokacin hada wannan rahoto, mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan jihar, ASP Mohammad Jalige, bai amsa kiransa ba ko kuma amsa sakon wayarsa.

Majiyar ta ce wadanda harin ya rutsa da su sun yi tattaki ne daga Birnin Gwari inda suka je Kano kafin masu garkuwar su tafi da su.

A cewarsa, wasu matafiya sun ga motocin da babu kowa a gefen hanya, inda ya kara da cewa maharan na shiga cikin dajin Yako mai firgita.

the punch newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naɗa shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...
X whatsapp