fidelitybank

‘Yan bindiga sun yi awon gaba da ‘yan kasuwar Kano da ba a tantance adadin su ba

Date:

Wasu ‘yan bindiga sun yi awon gaba da wasu ‘yan kasuwar Kano wadanda ba a tantance adadinsu ba, a kusa da dajin Ungwan Yako da ke karamar hukumar Birnin-Gwari ta jihar Kaduna a ranar Laraba.

Wata majiya ta bayyana cewa, ‘yan bindigar sun tare babbar hanyar ne a daidai lokacin da ‘yan kasuwar ke tafiya Kano daga Brinin Gwari inda a ke zargin su da kai wadanda harin ya rutsa da su zuwa wani wuri da ba a sani ba.

Hanyar Birin zuwa Gwari, a tsawon shekaru, ta zama tarkon mutuwa ga masu ababen hawa da matafiya, sakamakon munanan ayyukan ‘yan bindiga da su ka addabi hanyar, wadda ta kasance hanyar shiga yankin Kudu maso Yammacin kasar nan zuwa jihar Kaduna.

PUNCH ta rawaito cewa, wasu ‘yan bindiga sun kai hari kan ayarin motocin tare da yin awon gaba da ‘yan kasuwa sama da 70 daga Kano a kan hanyar Birnin Gwari zuwa Kaduna a ranar 22 ga Disamba, 2021.

Sai dai rundunar ‘yan sanda a Kaduna cikin kasa da sa’o’i 24, ta tattara tare da kubutar da 48 daga cikin wadanda lamarin ya shafa, yayin da wata mace da a ka kashe ba a san inda ta ke ba har zuwa yau.

Har yanzu dai ba a tabbatar da faruwar lamarin ba, ko dai daga gwamnatin jihar ko kuma rundunar ‘yan sandan jihar.

Har ya zuwa lokacin hada wannan rahoto, mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan jihar, ASP Mohammad Jalige, bai amsa kiransa ba ko kuma amsa sakon wayarsa.

Majiyar ta ce wadanda harin ya rutsa da su sun yi tattaki ne daga Birnin Gwari inda suka je Kano kafin masu garkuwar su tafi da su.

A cewarsa, wasu matafiya sun ga motocin da babu kowa a gefen hanya, inda ya kara da cewa maharan na shiga cikin dajin Yako mai firgita.

daily post today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp