Wasu da ake zargin ƴan bindiga ne sun kashe sama da mutune 20 a Galadima Kogo da ke Jihar Neja.
Wasu da suka shaida lamarin sun bayyana wa BBC cewa, ƴan bindigan sun je garin ne da tsakar ranar Asabar misalin ƙarfe biyu na rana kan babura da manyan makamai, inda suka buɗe wuta.
Bayan jama’ar da ƴan bindigar suka kashe akwai da dama waɗanda suka ji raunuka kamar yadda mazauna garin waɗanda suka tsira suka shaida wa BBC.
Rahotanni sun ce, an bindigar sun je ofishin ƴan sa kai sun kuɓutar da ƴan uwansu, sannan suka banka masa wuta tare da wasu motoci.
An ce ƴan bindigar sun shafe aƙalla sa’o’i uku suna buɗe wuta tare da ƙona gidajen jama’a.
Kwamishinan Ƙananan Hukumomi na Jihar Neja Emmanuel Umar ya tabbatar da kai harin, cewa har yanzu ba su kammala tantance adadin waɗanda aka kashe ba.