Rahotanni sun tabbatar da cewa wasu ‘yan bindiga sun yi kutse a wajen wani taron shugabannin jam’iyyar APC a karamar hukumar Enugu ta Kudu tare da bude musu
Rahotanni sun ce ‘yan bindigar kusan su bakwai sun kashe mutum biyu tare da raunata wasu da dama yayin da suka yi awon gaba da mutum daya daga cikin shugabannin na APC na mazaba ta uku ta unguwar Obeagu Awkunanaw a karamar hukumar Enugu ta Kudu.
Daya daga cikin wadanda ‘yan bindigar suka kashe shi ne, tsohon shugaban jam’iyyar na karamar hukumar na baya-bayan nan, wanda kuma shi ne mataimakin shugaban matasa na jan’iyyar na jihar a yanzu, mai suna, Kelvin Ezeoha, a cewar BBC.
Sai dai har kawo wannan lokacin ba a san ko harin na da nasaba da siyasa ba ko kuma hari ne na haramtacciyar kungiyar ‘yan aware ta Biyafara ba, IPOB, wadanda suke kai hare-hare a kan jama’a a yankin Kudu maso Gabas na Najeriya da sunan tabbatar da dokar zama a gida.
Zuwa lokacin hada wannan rahoton, rundunar ‘yan sanda ta jihar ta Enugu ba ta ce komai ba ko fitar da wata sanarwa dangane da harin.