fidelitybank

‘Yan Bindiga: An harbe wani Basarake a Ondo

Date:

Wasu ‘yan bindiga sun harbe wani babban basarake a masarautar Owo da ke jihar Ondo, Elerewe, Tunde Ilori.

Rahotanni na nuni da cewa an kashe Ilori ne a ranar Laraba a lokacin da ya ke dawowa da shi da wasu sarakuna bayan sun je sasanta wani rikicin a yankin.

Haka kuma ‘yan bindigar sun harbe wani basarake wanda har yanzu ba a bayyana sunan sa ba, kuma a halin yanzu yana samun kulawa a wata cibiyar lafiya da ke garin.

Wasu matasa da su ka fusata a garin da yammacin ranar Laraba sun gudanar da zanga-zanga tare da tare hanya da kona tayoyi a unguwar First Bank da ke Owo.

Gidan talabijin din Channels ya rawaito cewa, mai magana da yawun rundunar ’yan sandan Jihar Ondo, DSP Funmilayo Odunlami ta tabbatar da faruwar lamarin.

Ta ce,”A halin yanzu ‘yan sanda na gudanar da bincike a kan lamarin da nufin kamawa tare da gurfanar da wadanda suka yi kisan gilla a gaban kuliya”. Inji DSP Funmilayo.

legit com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naɗa shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...
X whatsapp