Gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello, ya bayyana aniyarsa na tsayawa takarar shugaban kasa a 2023, bayan babban taron jam’iyyar APC da aka shirya gudanarwa a wata mai zuwa.
A ranar 26 ga watan Fabrairu ne jam’iyya mai mulki za ta gudanar da babban taronta na kasa.
Bello, wanda ya bayyana hakan a wata tattaunawa da ya yi da manema labarai a Lokoja, bayan da wasu ‘yan Najeriya na gida da waje ke matsa masa lamba kan ya tsaya takarar shugabancin kasa a wani yunkuri na kara karfafa nasarorin da shugaba Muhammadu Buhari ya samu.
Ya ce: “Bisa umarni da kiran ‘yan Najeriya, matasan Najeriya da mata da jama’a a duk fadin duniya da ke kira na da in tsaya takara, domin in kara kaimi kan nasarar da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya samu. Tabbas zan amsa hakan bayan taron mu kamar yadda ya kasance.”
Gwamnan ya bayyana fatansa na cewa APC za ta kara zage bayan babban taron kasa.