fidelitybank

Wani babban al’amari zai faru a siyasar Kano da Najeriya – Kwankwaso

Date:

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran tafiyar darikar Kwankwasiyya, Sanata Rabiu Kwankwaso, ya gargadi mabiyansa da su yi taka tsan-tsan tare da daina adawa a kan yin sulhu da abokin hamayyar sa na siyasa da Gwamna Abdullahi Ganduje na jihar.

PlatinumPost ta rawaito cewa tun bayan ziyarar ta’aziyyar da gwamnan jihar Kano, Dr Abdullahi Umar Ganduje ya kai masa magoya bayan sa su ke ta tafo albarkacin bakin su a kai.

Ziyarar dai ta janyo cece-ku-ce kan cewa ’yan siyasar biyu da su ka rabu kai tsaye bayan zaben 2015, na gab da yin sulhu.

A cikin wani faifan bidiyo da a ke kyautata zaton Rahma TV ta dauka a lokacin da ta ke hira da Kwankwaso, abun ya sauya salo a siyasar Kano.

A cewarsa, jihar na karkata zuwa lokaci mafi muhimmanci a tarihin siyasarta, wanda ke bukatar zage-zage domin samun nasara, ya na mai kira ga mabiya Kwankwasiyya da su yi taka-tsan-tsan tare da daina adawa da sabbin matakan.

“Bari in yi amfani da wannan dama wajen gargadi mabiyanmu, wadanda ke cewa idan aka yi sulhu, za su fice daga jam’iyyar ko kuma kungiyar gaba daya.

”Ina gargadin su da su kiyaye kalaman su. Jihar mu ta na ganin sabon alfijir a tarihin siyasarta. Idan misali tafiyar siyasar mu mataki na 7 ne, to abin da zai biyo baya shi ne mataki na 6, zabe mai zuwa kuma shi ne mataki na 7. Wannan mataki na 7 shi ne mafi wahala da ke bukatar kwarewar siyasa da gogewa, domin cimma matsaya,” A cewar Kwankwaso.

Kwankwaso ya kara da cewa “Mu na gargadin mabiyan mu da su yi hattara kan wannan sabon babi a siyasar mu. Mutane ba sa yin furuci a kan abubuwan da ba su sa ni ba.

“Akwai wani babban al’amari da zai faru a siyasar Kano da ma Najeriya, domin haka ina gargadin mabiyan mu da su ba ta goyon baya, domin gudun yin nadama a lokacin da abin ya faru,” inji Kwankwaso.

Tsohon ministan ya kuma yi kira ga magoya bayansa da su ba shi shawara kan duk wani abu da su ke ganin bai dace ba, ya na mai ba da tabbacin cewa za a kirga kuri’unsu a sabuwar tafiyar siyasar jihar.

nigeria 
news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mu na aiki tuƙuru wajen daƙile ayyukan ta’adda a Najeriya – Christopher Musa

Babban hafsan tsaron Najeriya, Janar Christopher Musa, ya tabbatarwa...

Mayaƙan ISWAP sun harbe Manoma 23 a Borno

Rahotanni sun bayyana cewa ƙungiyar mayaƙan ISWAP ta kashe...

Real Madrid ta ɗauki ɗan wasan baya daga Bournemouth

Real Madrid ta sanar da sayen ɗan wasan baya...

Gwamnatin Kano ta haramta yin bikin Ƙauyawa da gidajen biki

Hukumar tace fina-finai a jihar Kano ta sanar da...

An kashe ƴan Boko Haram biyar a Borno

Dakarun sojin Najeriya haɗe da wasu maharba sun daƙile...

Farashin Shinkafa zai cigaba da sauka – BUA

Shugaban rukunin kamfanonin BUA, Abdul Samad Rabiu, ya alƙawarta...

An kashe mutane 10 a wani sabon rikici da ya ɓarke a Filato

Aƙalla mutabe 10 ne aka kashe tare da sace...

Duk da sauƙin da aka samu har yanzu Abuja na fuskantar hauhawar farashi

Duk da cewa hukumar ƙididdiga ta ƙasa NBS, ta...

Hauhawar farashi ya ragu da kaso 23.71 a Najeriya – NBS

An samu raguwar hauhawar farashin kayayyaki a Najeriya daga...

Fiye da mutane 100 Makiyaya aka kashe a Jos

An ruwaito cewa an kashe wani makiyayi guda da...

Tinubu ka kori shugaban JAMB – Sowore

Dan siyasa mai fafutuka, Omoyele Sowore, ya yi kira...

Majalisa ta yi watsi da ƙudirin karɓa-karɓa

Majalisar wakilai ta yi watsi da wani ƙudirin doka...
X whatsapp