fidelitybank

Rikicin Siyasa: Malam Ibrahim ya ficce daga jam’iyar APC

Date:

Fitaccen malamin addinin musulunci kuma shugaban majalisar malamai ta Kano, Sheikh Ibrahim Khalil ya bayyana ficewarsa daga jam’iyyar APC.

Da alama dai rikicin da ya dabaibaye jam’iyyar APC reshen jihar Kano na yin mummunan tasiri a jam’iyyar yayin a cikin ‘yan kwanakin nan tun bayan da a ka fara samun tsagin shugabanci a cikin jam’iyar.

Malam Ibrahim ya bayyana ficewarsa daga cikin jam’iyar APC a cikin zantawarsa da BBC.

Ya ce,“To, a matsayina na dan APC kuma daya daga cikin dattawa kuma daya daga cikin jiga-jigan jam’iyyar, ina so na tabbatar na fice daga APC,” kamar yadda ya shaida wa BBC.

“Komai na rayuwa ya na da dalili. Dalilai uku ne: ko dai mai ilimi da hankali ya sa ni, ko kuma kowa ya sa ni, ko kuma shi kansa ya san dalili”.

Ya ce ficewar sa daga jam’iyyar ba ta da alaka da zargin da a ke yi masa na tsige shi a matsayin shugaban Majalisar Malamai.

“Idan da haka ne, da na sauka daga mulki. Ba dalili ba ne, domin kamar yadda ban yi bayanin rabuwata da gwamnati ba, ba sai na bata lokaci wajen bayyana ta ba.

“Ban daina siyasa ba kuma ban ce ba zan shiga jam’iyyar ba. Ni da kaina ban shiga ANPP ba, magoya bayana ne su ka yi min rajista. Domin haka yanzu zan shiga jam’iyyar da na ke so da kaina,” inji Malam Ibrahim Khalil.

sun newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za mu ɗauki matakin hana sake faruwar kisan mutane – Gwamnatin Filato

Gwamnatin jihar Filato ta jaddada aniyarta ta ɗaukar mataki...

Babu barazanar tsaro a Abuja – Najeriya

Gwamnatin Tarayya ta ce, babu wata barazanar a babban...

Isra’ila za ta mayarwa da Iran martani duk da tsagaita wuta

Ministan tsaron Isra'ila, Katz ya bayyana cewa, ya ba...

Ba mu kai wa Isra’ila hari ba – Iran

Kafar watsa labarai ta Iran ta ruwaito gwamnatin ƙasar...

Duk da faduwar farashin mai NNPCL ya kara farashi

Kamfanin man fetur na Najeriya, NNPCL ya ƙara farashin...

Duk wasu ƙawayen Amurka za su ɗanɗanar kuɗarsu – Iran

Rundunar dakarun juyin juya halin Iran ta fitar da...

Iran ta mayar da martani kan sojojin Amurka dake Qatar

Kafofin yaɗa labaran Iran sun bayyana cewa ƙasar ta...

Faransa ba ta goyon bayan Amurka na kifer da gwamnatin Iran – Barrot

Ministan harkokin wajen Faransa ya ce, ƙasarsu ba ta...

Kotu a Kano ta ɗaure masu satar Yara

Babbar kotun jihar Kano da ke zamanta a Miller...

Ba wata hujja da Amurka za ta kai wa Iran hari – Rasha

An gudanar da tattaunawa tsakanin shugaban Rasha Vladimir Putin...

Tinubu ya miƙa saƙon ta’aziyya ga mutanen Kano da Kaduna da Borno

Shugaba Bola Tinubu ya yi Alla-wadai da kisan wasu...

Amurka ta tafka babban kuskure – Iran

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya yi Alla-wadai...
X whatsapp