fidelitybank

Turji: Shugaban ‘yan ta’adda ya samu mummunan raunika a harin soji

Date:

Shahararren shugaban ‘yan ta’addan, Bello Turji, ya samu munanan raunuka a lokacin da jiragen yakin sojoji su ka kai farmaki maboyar sa da kuma sansanonin ‘yan bindiga a yankin Arewa maso Yamma.

PRNigeria ta rawaito cewa, harin da jiragen yakin rundunar sojin sama, ATF, Operation Hadarin Daji su ka kai, sun kuma kashe ‘yan ta’adda da dama, a wani samame da su ka kai a wasu dazuzzukan jihohin Zamfara da Sokoto, da sanyin safiyar Asabar.

Wata majiyar leken asiri ta soji ta bayyana cewa, farmakin da rundunar sojin sama ta kai tare da hadin gwiwar sojojin kasa na sojojin Najeriya, an kai harin ne a garin Shinkafi da ke Zamfara da Bafarawa da Isa a yankin Sabon Birni a jihar Sokoto.

A cewar majiyar leken asirin, ba a iya tantance ainihin adadin ‘yan ta’addan da aka kawar da su a hare-haren ta sama, a cikin aikin wayewar gari.

Sai dai rahotanni na nuni da cewa, wasu ‘yan ta’addan da su ka samu munanan raunuka sun yi yunkurin guduwa, amma dakarun kasa sun yi musu kwanton bauna.

Baya ga wani samame na kwatsam a Katsina da Zamfara, daga ranar 16 da 17 ga Disamba, 2021, jiragen NAF sun kai hare-hare a sansanonin ‘yan bindiga a yankin Isa, Sabon Birni da kuma Gabashin Tozei inda aka yi nasarar fatattakar ‘yan bindiga da dama yayin da wasu suka tsere cikin rudani.

Bugu da kari a safiyar ranar 18 ga watan Disamba, an kai hare-hare ta sama a kauyen Gebe da ke jihar Sokoto, inda har yanzu ‘yan bindigar suka ci zarafin jama’a da ba su ji ba gani ba. Amma duk da haka, kadan daga cikin ‘yan fashin ne suka tsere, suka bar makamansu, a cikin wannan tsar. Cewar majiyar inji majiyar.

legitnewsnigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An sake mayar da yan Najeriya 294 gida daga Nijar

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta Najeriya Nema ta...

An gano motoci 35 da aka sace a wata shida

Hukumar kiyaye haɗurra ta ƙasa a Najeriya ta ce...

Shugaban Laberiya ya je ta’aziyyar Buhari a Monrovia

Shugaban Ƙsaar Laberiya Joseph Nyuma Boakai ya kai ziyarar...

Rundunar Yansandan Kaduna ta hana gangamin goyon bayan Peter Obi

Rundunar 'yansandan Najeriya reshen jihar Kaduna ta hana gudanar...

Iran ta zartar da hukuncin kisa a kan Mutane 3

Hukumomi a Iran sun zartar wa mutum uku hukuncin...

Ƴansanda sun kama ƙasurgumin ɗanbindiga a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna ta ce, jami'an ta sun...

Sudan ta Kudu ta yi ta’aziyyar Buhari

Mukaddashin Ministan Harkokin Wajen Sudan ta Kudu, Ambasada Akuei...

Trump ya na fama da cuta mai kumbura kafa da toshewar hanyar jini

A ranar Alhamis ne Fadar White House ta sanar...

Yadda aka gudanar da addu’o’in Buhari a Villa

A ranar Alhamis ne aka gudanar da addu'o'i ga...

Rasha tarnaki ce a wajen Tarayyar Turai – Jamus

Shugaban gwamnatin Jamus Friedrich Merz ya shaidawa BBC cewa...

Amurka ba ta goyon bayan Isra’ila a harin Syria – Trump

Amurka ta ce ba ta goyon bayan hare-haren da...

Tinubu zai zo Kano ta’aziyyar Dantata

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu zai kai ziyara Kano yau...
X whatsapp