fidelitybank

Turji: Shugaban ‘yan ta’adda ya samu mummunan raunika a harin soji

Date:

Shahararren shugaban ‘yan ta’addan, Bello Turji, ya samu munanan raunuka a lokacin da jiragen yakin sojoji su ka kai farmaki maboyar sa da kuma sansanonin ‘yan bindiga a yankin Arewa maso Yamma.

PRNigeria ta rawaito cewa, harin da jiragen yakin rundunar sojin sama, ATF, Operation Hadarin Daji su ka kai, sun kuma kashe ‘yan ta’adda da dama, a wani samame da su ka kai a wasu dazuzzukan jihohin Zamfara da Sokoto, da sanyin safiyar Asabar.

Wata majiyar leken asiri ta soji ta bayyana cewa, farmakin da rundunar sojin sama ta kai tare da hadin gwiwar sojojin kasa na sojojin Najeriya, an kai harin ne a garin Shinkafi da ke Zamfara da Bafarawa da Isa a yankin Sabon Birni a jihar Sokoto.

A cewar majiyar leken asirin, ba a iya tantance ainihin adadin ‘yan ta’addan da aka kawar da su a hare-haren ta sama, a cikin aikin wayewar gari.

Sai dai rahotanni na nuni da cewa, wasu ‘yan ta’addan da su ka samu munanan raunuka sun yi yunkurin guduwa, amma dakarun kasa sun yi musu kwanton bauna.

Baya ga wani samame na kwatsam a Katsina da Zamfara, daga ranar 16 da 17 ga Disamba, 2021, jiragen NAF sun kai hare-hare a sansanonin ‘yan bindiga a yankin Isa, Sabon Birni da kuma Gabashin Tozei inda aka yi nasarar fatattakar ‘yan bindiga da dama yayin da wasu suka tsere cikin rudani.

Bugu da kari a safiyar ranar 18 ga watan Disamba, an kai hare-hare ta sama a kauyen Gebe da ke jihar Sokoto, inda har yanzu ‘yan bindigar suka ci zarafin jama’a da ba su ji ba gani ba. Amma duk da haka, kadan daga cikin ‘yan fashin ne suka tsere, suka bar makamansu, a cikin wannan tsar. Cewar majiyar inji majiyar.

the sun newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp