fidelitybank

Turji: Shugaban ‘yan ta’adda ya samu mummunan raunika a harin soji

Date:

Shahararren shugaban ‘yan ta’addan, Bello Turji, ya samu munanan raunuka a lokacin da jiragen yakin sojoji su ka kai farmaki maboyar sa da kuma sansanonin ‘yan bindiga a yankin Arewa maso Yamma.

PRNigeria ta rawaito cewa, harin da jiragen yakin rundunar sojin sama, ATF, Operation Hadarin Daji su ka kai, sun kuma kashe ‘yan ta’adda da dama, a wani samame da su ka kai a wasu dazuzzukan jihohin Zamfara da Sokoto, da sanyin safiyar Asabar.

Wata majiyar leken asiri ta soji ta bayyana cewa, farmakin da rundunar sojin sama ta kai tare da hadin gwiwar sojojin kasa na sojojin Najeriya, an kai harin ne a garin Shinkafi da ke Zamfara da Bafarawa da Isa a yankin Sabon Birni a jihar Sokoto.

A cewar majiyar leken asirin, ba a iya tantance ainihin adadin ‘yan ta’addan da aka kawar da su a hare-haren ta sama, a cikin aikin wayewar gari.

Sai dai rahotanni na nuni da cewa, wasu ‘yan ta’addan da su ka samu munanan raunuka sun yi yunkurin guduwa, amma dakarun kasa sun yi musu kwanton bauna.

Baya ga wani samame na kwatsam a Katsina da Zamfara, daga ranar 16 da 17 ga Disamba, 2021, jiragen NAF sun kai hare-hare a sansanonin ‘yan bindiga a yankin Isa, Sabon Birni da kuma Gabashin Tozei inda aka yi nasarar fatattakar ‘yan bindiga da dama yayin da wasu suka tsere cikin rudani.

Bugu da kari a safiyar ranar 18 ga watan Disamba, an kai hare-hare ta sama a kauyen Gebe da ke jihar Sokoto, inda har yanzu ‘yan bindigar suka ci zarafin jama’a da ba su ji ba gani ba. Amma duk da haka, kadan daga cikin ‘yan fashin ne suka tsere, suka bar makamansu, a cikin wannan tsar. Cewar majiyar inji majiyar.

legit.ng.news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...
X whatsapp