Gwamna jihar Kaduna, Nasir El-Rufai ya mika sakonta’azziya ga iyalan wadanda harin ‘yan ta’adda ya rutsa da su tare da yi musu addu’ar Allah ya jikan su,
Gwamnan ya kuma jajanta wa al’ummar da abin ya shafa, ya kuma umurci hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar Kaduna da ta gudanar da tantancewar cikin gaggawa a yankin domin bayar da agaji.
Kwamishinan Ma’aikatar Tsaro da Harkokin Cikin Gida ta Jihar Kaduna, Samuel Aruwan, ya sanar da hakan cewa, hukumomin tsaro na Soja da ‘yan sanda su ka kai wa Gwamnatin Jihar Kaduna rahoton cewa, an kashe mutane sama da 20 a harin da ‘yan ta’adda su ka kai wasu kauyukan karamar hukumar Giwa.
Za kuma a tantance sunayen wadanda a ka kashe da zarar an tabbatar da karin bayani daga gwamnatin jihar Kaduna. A halin yanzu, wanda jami’an tsaro sun ci gaba da sintiri a yankin baki daya,
A cewar rahoton, ‘yan ta’adda sun kai hari a kauyukan Kauran Fawa da Marke da Riheya da ke Idasu, a karamar hukumar Giwa, inda su ka kashe mutane sama da 20 har zuwa lokacin da a ka samu labarin.