fidelitybank

Kungiyar tsofaffin dalibai ta BIKOBA ta yi sababbin jagorori

Date:

Kungiyar tsofaffin dalibai na Birnin Kudu BIKOBA, ta gudanar da babban taronta na shekara-shekara tare da zabar sabbin shugabannin da za su tafiyar da harkokin kungiyar nan da shekaru Uku masu zuwa.

Da ya ke gabatar da jawabin bankwana a wurin taron da a ka gudanar a harabar dakin karatu na Murtala Muhammad da ke Kano, shugaban mai barin gado Pharmacist Nuhu Isa Abdullahi, ya ce,”Babban kalubalen da su ka fuskanta a lokacin gwamnatinsu shi ne samar da ruwan sha a makarantar, a lokacin gudanar da aikin mu an gina rijiyar burtsatse mai amfani da hasken rana tare da karin rijiyoyin famfo guda Uku wanda hakan ya magance matsalar karancin ruwa a makarantar”.

Sababbin zababbun shugabannin BIKOBA su ne:

Ja’afar, Usman, Turakin Gaya, na class 1966 a ka zabe shi a matsayin shugaban kasa.

Sani Ibrahim Khalid, mataimakin kungiyar na I

Sale Ibrahim Dawakin Kudu, mataimaki na II

Sakatare Umar Garba Kabara, a matsayin Sakatare

An zabi Maje Kurawa mataimakin Sakatare

Attahiru Gwangwazo ma’aji

An kuma zabi Mahmud Ibrahim Kwari a matsayin sakataren yada labarai, yayin da Abdurrahman Na’iya ya zama sakataren yada labarai.

Sauran sun hadar da Usman Garba a matsayin sakataren kudi da mataimakin sakataren yada labarai, Muahmmad Sani da kuma mai binciken kudi Bala Baba Zandam.

A jawabinsa na karrama sabon zababben shugaban kungiyar BIKOBA, Alhaji Ja’afar Sani Turakin Gaya na aji 1966 ya yi alkawarin tafiya da kowa da kowa kuma ya yi alkawarin ba zai kyale su ba.

Alhaji Jaafar Sani ya ce,”BIKOBA ta zama babban iyali mun dauki matakin tabbatar da cewa mun yi aiki tare”.

A nasa jawabin gwamnan jihar Kano Dr. Abdullahi Umar Ganduje wanda ya samu wakilcin sakataren gwamnatin jihar, Alhaji Usman Alhaji,ya ce,”BIKOBA mun bi mataki mai kyau wajen zaben shugabanninta. Gwamnan ya bukaci sabbin zababbun shugabannin da su fi na magabatan su aiki sosai”. A cewar NigerianTracker.

 

 

punch newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mun ceto tsohuwa ƴar shekaru 80 daga masu garkuwa – Ƴansanda

Rundunar ƴansandan jihar Jigawa, ta ce ta ceto wata...

APC na taron kasu ruwa da tsaki

Jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya za ta gudanar da...

Matatar Ɗangote ta sake karya farashin fetur

Kamfanin Dangote da ya mallaki matatar mai ta Dangote...

Idan Isra’ila ta kai mana hari Amurka ce – Iran

Ministan harkokin wajen ƙasar Iran ya ce, gwamnatin Tehran...

Kotu ta daure mai kiwon Akuya bayan ta cinye shukokin gwamnatin Kano

Wata kotun majistare da ke Kano ta daure wasu...

‘Yansanda sun dakile yi garkuwa da mutane a Katsina

Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina ta dakile wani yunkurin...

‘Yansanda sun dakume ‘Yan Fashi uku a Kano

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta kama wasu ‘yan...

Jarumar Nollywood ta zama sojan ruwar Amurka

Fitacciyar jarumar nan ta Najeriya Grace Bassey wacce a...

Na yi takaicin barin Ancelloti daga Real Madrid – Carvajal

Dan wasan baya na kungiyar kwallon kafa ta Real...

Mu na shirin yin kawancen jam’iyya – PDP

Majalisar dattawa ta jam'iyyar PDP, ta bayyana shirin jam'iyyar...

Ana zanga-zanga a Binuwai sakamakon harbe Dalibi dan shekara 23

Wata zanga-zanga ta barke a Makurdi, babban birnin jihar...

A na cigaba da farautar Fursunonin Osun da suka tsere

Hukumar gyaran hali ta Najeriya (NCoS) ta ce, ta...
X whatsapp