Kungiyar tsofaffin dalibai na Birnin Kudu BIKOBA, ta gudanar da babban taronta na shekara-shekara tare da zabar sabbin shugabannin da za su tafiyar da harkokin kungiyar nan da shekaru Uku masu zuwa.
Da ya ke gabatar da jawabin bankwana a wurin taron da a ka gudanar a harabar dakin karatu na Murtala Muhammad da ke Kano, shugaban mai barin gado Pharmacist Nuhu Isa Abdullahi, ya ce,”Babban kalubalen da su ka fuskanta a lokacin gwamnatinsu shi ne samar da ruwan sha a makarantar, a lokacin gudanar da aikin mu an gina rijiyar burtsatse mai amfani da hasken rana tare da karin rijiyoyin famfo guda Uku wanda hakan ya magance matsalar karancin ruwa a makarantar”.
Sababbin zababbun shugabannin BIKOBA su ne:
Ja’afar, Usman, Turakin Gaya, na class 1966 a ka zabe shi a matsayin shugaban kasa.
Sani Ibrahim Khalid, mataimakin kungiyar na I
Sale Ibrahim Dawakin Kudu, mataimaki na II
Sakatare Umar Garba Kabara, a matsayin Sakatare
An zabi Maje Kurawa mataimakin Sakatare
Attahiru Gwangwazo ma’aji
An kuma zabi Mahmud Ibrahim Kwari a matsayin sakataren yada labarai, yayin da Abdurrahman Na’iya ya zama sakataren yada labarai.
Sauran sun hadar da Usman Garba a matsayin sakataren kudi da mataimakin sakataren yada labarai, Muahmmad Sani da kuma mai binciken kudi Bala Baba Zandam.
A jawabinsa na karrama sabon zababben shugaban kungiyar BIKOBA, Alhaji Ja’afar Sani Turakin Gaya na aji 1966 ya yi alkawarin tafiya da kowa da kowa kuma ya yi alkawarin ba zai kyale su ba.
Alhaji Jaafar Sani ya ce,”BIKOBA ta zama babban iyali mun dauki matakin tabbatar da cewa mun yi aiki tare”.
A nasa jawabin gwamnan jihar Kano Dr. Abdullahi Umar Ganduje wanda ya samu wakilcin sakataren gwamnatin jihar, Alhaji Usman Alhaji,ya ce,”BIKOBA mun bi mataki mai kyau wajen zaben shugabanninta. Gwamnan ya bukaci sabbin zababbun shugabannin da su fi na magabatan su aiki sosai”. A cewar NigerianTracker.