fidelitybank

Tsaro: ‘Yan ta’adda sun kashe mutane sama da 20 a Kaduna – Hukumomi

Date:

Gwamna jihar Kaduna, Nasir El-Rufai ya mika sakonta’azziya ga iyalan wadanda harin ‘yan ta’adda ya rutsa da su tare da yi musu addu’ar Allah ya jikan su,

Gwamnan ya kuma jajanta wa al’ummar da abin ya shafa, ya kuma umurci hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar Kaduna da ta gudanar da tantancewar cikin gaggawa a yankin domin bayar da agaji.

Kwamishinan Ma’aikatar Tsaro da Harkokin Cikin Gida ta Jihar Kaduna, Samuel Aruwan, ya sanar da hakan cewa, hukumomin tsaro na Soja da ‘yan sanda su ka kai wa Gwamnatin Jihar Kaduna rahoton cewa, an kashe mutane sama da 20 a harin da ‘yan ta’adda su ka kai wasu kauyukan karamar hukumar Giwa.

Za kuma a tantance sunayen wadanda a ka kashe da zarar an tabbatar da karin bayani daga gwamnatin jihar Kaduna. A halin yanzu, wanda jami’an tsaro sun ci gaba da sintiri a yankin baki daya,

A cewar rahoton, ‘yan ta’adda sun kai hari a kauyukan Kauran Fawa da Marke da Riheya da ke Idasu, a karamar hukumar Giwa, inda su ka kashe mutane sama da 20 har zuwa lokacin da a ka samu labarin.

legits news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...
X whatsapp