fidelitybank

Tsaro: ‘Yan Katsina ku mallaki Bindigar kan ku -Masari

Date:

Gwamnan jihar Katsina, Aminu Bello Masari, ya ja hankalin al’ummar jihar da su yi amfani da makamai domin tunkarar ‘yan bindiga da ke addabar su.

A cewar gwamnan yayin zantawa da manema labarai ya ce, jami’an tsaro kadai ba za su iya magance matsalar rashin tsaro a jihar ba.

Da ya ke jawabi yayin wani taron manema labarai a Katsina, Masari ya jaddada cewa yawan jami’an tsaro a jihar bai isa a shawo kan lamarin ba.

“A Musulunci ya halatta mutum ya kare kansa daga harin. Dole ne mutum ya tashi ya kare kansa, da iyalansa, da dukiyarsa. Idan ka mutu ka na ƙoƙarin kare kanka, za a ɗauke ka a matsayin shahidi. Abin mamaki ne yadda dan fashi zai mallaki bindiga alhali mutumin kirki da ke kokarin kare kansa da iyalansa ba shi da ita”.

Ya kuma yi nuni da cewa gwamnatin jihar za ta taimaka wa masu shirin mallakar makamai, domin kawo karshen matsalar ‘yan fashi da makami a jihar.

“Za mu goyi bayan wadanda su ka zo da shirin sayo makamai, saboda mazauna yankin na bukatar su kara kaimi ga kokarin hukumomin tsaro. Wadannan mutane (jami’an tsaro) ba su da yawan da za su kare jama’a.

“Lokacin da Shugaba Buhari ya zo, har ma ya yi kokarin kara yawan jami’an tsaron mu, amma abin bai wadatar ba. Ku lissafa kanku, ‘yan sanda nawa mu ke da su a kasar nan? Sojoji nawa mu ke da su?

“Ko da mu ka ce kowane dan sanda ya koma jiharsa, ba zai wadatar ba. Domin haka, idan mu ka ninke hannu mu ka yanke shawarar yin komai, za mu fi shan wahala”. Inji shi.

Masari ya ce,”‘Yan sanda za su yi rijistar duk bindigogin da mazauna garin su ka saya, domin tabbatar da an yi amfani da su yadda ya kamata. Katsina, kamar sauran jihohin Arewa maso Yamma, Zamfara, Kaduna, Sokoto, da Kebbi, sun sha fama da hare-haren kungiyoyin ‘yan ta’adda”. A cewar Masari

Rahotanni na nuni da cewa, Daruruwan mutane ne a ka kashe ko kuma a ka yi garkuwa da su a Katsina cikin wannan shekara tare da raba dubbai daga gidajen su.

 

legit news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojojin hadin gwiwa sun hallaka ‘yan Boko Haram a tafkin Chadi

Rundunar hadin gwiwa mai yaƙi da Boko Haram a...

Na yi rashin aboki na gari kuma Najeriya ta rasa mutumin kirki – Tinubu

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, na ci gaba da alhinin...

Shettima ya jagoranci yi wa Buhari addu’o’i na musamman a Daura

An gudanar da addu'o'i na musamman don neman gafara...

Isra’ila ta kashe mana fararen hula – Syria

Shugaban Syria, Ahmed al-Sharaa ya zargi Isra'ila da kai...

Za mu koma fadar gwamnatin Katsina mu karbi gaisuwar Buhari – Radda

Gwamnan jihar Katsina, Dikko Umar Radda ya ce bayan...

Tinubu zai jagoranci yi wa Buhari addu’a

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, zai jagoranci taron addu'o'i na...

Muƙarraban Buhari sun ci amanar da ya ba su lokacin mulkinsa – Bagos

Wani tsohon ɗan majalisar wakilai, Dachung Bagos ya bayyana...

Guardiola ya bude kofa ga ‘yan wasa shida su bar kungiyar

Kocin Manchester City, Pep Guardiola, a shirye yake ya...

Ba gudu ba ja da baya a zanga-zangar mu – Tsofaffin ‘Yansanda

Kungiyar ‘yan sandan Najeriya masu ritaya ta sanar da...

Malami ya magantu kan sukar rashawa a mulkin marigayi Buhari

Tsohon babban Lauyan Najeriya kuma ministan shari'a, Abubakar Malami,...

Turkiyya ta gargadi Najeriya kan ‘yan ta’addar FETO

Gwamnatin Turkiyya ta fitar da wani gargadin cewa, mambobin...

Kiristoci sun jinjinawa Musulmai yadda aka yi jana’izar Buhari ba kashe kudi

Ana samun karuwar al’ummar Kudancin Najeriya musamman mabiya addinin...
X whatsapp