fidelitybank

Tsaro: ‘Yan Katsina ku mallaki Bindigar kan ku -Masari

Date:

Gwamnan jihar Katsina, Aminu Bello Masari, ya ja hankalin al’ummar jihar da su yi amfani da makamai domin tunkarar ‘yan bindiga da ke addabar su.

A cewar gwamnan yayin zantawa da manema labarai ya ce, jami’an tsaro kadai ba za su iya magance matsalar rashin tsaro a jihar ba.

Da ya ke jawabi yayin wani taron manema labarai a Katsina, Masari ya jaddada cewa yawan jami’an tsaro a jihar bai isa a shawo kan lamarin ba.

“A Musulunci ya halatta mutum ya kare kansa daga harin. Dole ne mutum ya tashi ya kare kansa, da iyalansa, da dukiyarsa. Idan ka mutu ka na ƙoƙarin kare kanka, za a ɗauke ka a matsayin shahidi. Abin mamaki ne yadda dan fashi zai mallaki bindiga alhali mutumin kirki da ke kokarin kare kansa da iyalansa ba shi da ita”.

Ya kuma yi nuni da cewa gwamnatin jihar za ta taimaka wa masu shirin mallakar makamai, domin kawo karshen matsalar ‘yan fashi da makami a jihar.

“Za mu goyi bayan wadanda su ka zo da shirin sayo makamai, saboda mazauna yankin na bukatar su kara kaimi ga kokarin hukumomin tsaro. Wadannan mutane (jami’an tsaro) ba su da yawan da za su kare jama’a.

“Lokacin da Shugaba Buhari ya zo, har ma ya yi kokarin kara yawan jami’an tsaron mu, amma abin bai wadatar ba. Ku lissafa kanku, ‘yan sanda nawa mu ke da su a kasar nan? Sojoji nawa mu ke da su?

“Ko da mu ka ce kowane dan sanda ya koma jiharsa, ba zai wadatar ba. Domin haka, idan mu ka ninke hannu mu ka yanke shawarar yin komai, za mu fi shan wahala”. Inji shi.

Masari ya ce,”‘Yan sanda za su yi rijistar duk bindigogin da mazauna garin su ka saya, domin tabbatar da an yi amfani da su yadda ya kamata. Katsina, kamar sauran jihohin Arewa maso Yamma, Zamfara, Kaduna, Sokoto, da Kebbi, sun sha fama da hare-haren kungiyoyin ‘yan ta’adda”. A cewar Masari

Rahotanni na nuni da cewa, Daruruwan mutane ne a ka kashe ko kuma a ka yi garkuwa da su a Katsina cikin wannan shekara tare da raba dubbai daga gidajen su.

 

punch news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...
X whatsapp